Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
Published: 18th, September 2025 GMT
Hukumar bunkasa ilimin gaba da sakandare ta jihar Jigawa ta shirya taron tattaunawa ga jami’an gudanar da shirin koyawa dalibai musamman wadanda suke da nakasu a jarrabawar NECO ko WAEC wato Remedial program don su sami nasarar cin jarrabawar da za ta basu damar ci gaba da karatu a makarantun gaba da sakandare.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban hukumar, Dr Abbas A Abbas ya bayyana cewar gwamnatin jihar jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta sahalewa hukumar gudanar da shirin da ta saba yi duk shekara wajen baiwa daliban da suka fadi a jarrabawar NECO ko WAEC koyarwa ta musamman.
Yana mai cewar, sahalewar na da nufin basu damar sake rubuta jarrabawar don su sami dukkanin abun da ake bukata da zai basu damar ci gaba da karatun gaba da sakandare.
Dr Abbas A Abbas yace wannan shirn daya ne daga irin shirye shiye guda 6 da hukumar ke gudanarwa wanda doka ta basu dama.
Ya kuma kara da cewar, makasudin wannan tattaunawar shine a zaburar da jami’an kan irin aikin dake gaban su na ilimantar da dalibai hanyoyin da za su bi wajen amsa tambayoyin da akeyi a jarrabawar NECO ko WAEC.
Yace hakance tasa hukumar ta gayyato kwararrun masana don su kara bayar da bita ga jami’an a fannonin jarrabawar da ta shafi turanci da lissafi da kuma irin kalubalen da dalibai kan fuskanta wajen amsa tambayoyin alokacin jarrabawa.
Dr Abass ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi wajen kokarin sa na bunkasa harkar ilimi wanda daya ne daga cikin kudure kuduren sa 12 na ciyar da jihar gaba.
A jawaban su daban daban, kwararriya mai baiwa Gwamna shawara a Basic Education, Dr Hauwa Mustapha Babura da mataimaki na musamman ga Gwamna a fannin ilimin manya, Alhaji Garba Makama Gwaram sun yabawa Gwamna Namadi bisa kokarin sa na tallafawa shirin da sauran shirye-shiryen da hukumar bunkasa ilimin manya ke gudanarwa don baiwa daliban da suka fadi a jarrabawa damar sanin makamar da za su sami damar sake yin wata jarrabawar.
Sun kuma yi kira ga Jami’an da zasu gudanar da shirin da su saka tsoron Allah da kishin taimakawa daliban don cimma nasarar da aka sa a gaba.
Kazalika, sun yabawa kokarin Baban sakataren gudanarwa na hukumar Dr Abbas A Abbas bisa jajircewar sa wajen habaka ilimin manya a fadin jihar Jigawa.
Radio Nigeria ya bamu rahoton cewar, a lokacin taron an gudanar da takardu daban-daban a kan sabbin dabarun da za’a bi don tallafawa daliban da basu damar sake rubuta jarrabawar musamman a fannin turanci da lissafi da kuma shawarwariin da za ayi amfani dssu don kwalliya ta biya kufin sabulu.
Fiye da jami’ai masu hiror da dalibai 131 ne da aka gayyata daga kananan hukumomi 26 suka halarci taron da aka gudanar a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake cikin sakatariyar jihar jigawa.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Manyan Makarantu a jarrabawar
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4mWaɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.
Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).
Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.
Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.
Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”
Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.
Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.
Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.
Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.
A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.
Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.