Hukumar bunkasa ilimin gaba da sakandare ta jihar Jigawa ta shirya taron tattaunawa ga jami’an gudanar da shirin koyawa dalibai musamman wadanda suke da nakasu a jarrabawar NECO ko WAEC wato Remedial program don su sami nasarar cin jarrabawar da za ta basu damar ci gaba da karatu a makarantun gaba da sakandare.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban hukumar, Dr Abbas A Abbas ya bayyana cewar gwamnatin jihar jigawa karkashin jagorancin Malam Umar Namadi ta sahalewa hukumar gudanar da shirin da ta saba yi duk shekara wajen baiwa daliban da suka fadi a jarrabawar NECO ko WAEC koyarwa ta musamman.

Yana mai cewar, sahalewar na da nufin basu damar sake rubuta jarrabawar don su sami dukkanin abun da ake bukata da zai basu damar ci gaba da karatun gaba da sakandare.

Dr Abbas A Abbas yace wannan shirn daya ne daga irin shirye shiye guda 6 da hukumar ke gudanarwa wanda doka ta basu dama.

Ya kuma kara da cewar, makasudin wannan tattaunawar shine a zaburar da jami’an kan irin aikin dake gaban su na ilimantar da dalibai hanyoyin da za su bi wajen amsa tambayoyin da akeyi a jarrabawar NECO ko WAEC.

Yace hakance tasa hukumar ta gayyato kwararrun masana don su kara bayar da bita ga jami’an a fannonin jarrabawar da ta shafi turanci da lissafi da kuma irin kalubalen da dalibai kan fuskanta wajen amsa tambayoyin alokacin jarrabawa.

Dr Abass ya kuma yabawa Gwamna Umar Namadi wajen kokarin sa na bunkasa harkar ilimi wanda daya ne daga cikin kudure kuduren sa 12 na ciyar da jihar gaba.

A jawaban su daban daban, kwararriya mai baiwa Gwamna shawara a Basic Education, Dr Hauwa Mustapha Babura da mataimaki na musamman ga Gwamna a fannin ilimin manya, Alhaji Garba Makama Gwaram sun yabawa Gwamna Namadi bisa kokarin sa na tallafawa shirin da sauran shirye-shiryen da hukumar bunkasa ilimin manya ke gudanarwa don baiwa daliban da suka fadi a jarrabawa damar sanin makamar da za su sami damar sake yin wata jarrabawar.

Sun kuma yi kira ga Jami’an da zasu gudanar da shirin da su saka tsoron Allah da kishin taimakawa daliban don cimma nasarar da aka sa a gaba.

Kazalika, sun yabawa kokarin Baban sakataren gudanarwa na hukumar Dr Abbas A Abbas bisa jajircewar sa wajen habaka ilimin manya a fadin jihar Jigawa.

Radio Nigeria ya bamu rahoton cewar, a lokacin taron an gudanar da takardu daban-daban a kan sabbin dabarun da za’a bi don tallafawa daliban da basu damar sake rubuta jarrabawar musamman a fannin turanci da lissafi da kuma shawarwariin da za ayi amfani dssu don kwalliya ta biya kufin sabulu.

Fiye da jami’ai masu hiror da dalibai 131 ne da aka gayyata daga kananan hukumomi 26 suka halarci taron da aka gudanar a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake cikin sakatariyar jihar jigawa.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Manyan Makarantu a jarrabawar

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.

Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.

Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.

“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.

Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.

Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jigawa Za Ta Shirya Taron Bita Na Musamman Ga Jami’anta
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya