A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya
Published: 29th, August 2025 GMT
Ba wai muna yin jayya da sanarar da ofishin Nuhu ya samu a tsakanin wadannan watanni ba ne kuma muna sane da kokarin da yake yi, na ganin cewa, ‘yan Nijeriya na samu su kwanta su yi barcin dare, idanuwansu biyu a rufe ba tare da wata fargabar ko za a kai masu hari ba.
Tabbas, muna jinjina masa kan yunkurin da yake ci gaba da yi na rage kalubalen rashin tsaro da Gwamnatin mai ci ta gada.
Amma mummunan harin da wasu mahara suka kai a watannin baya a yankin Yelwata, inda suka yi wa wasu al’umomin yankin kisan kiyashi da kuma harin da ‘yan bindiga suka kai kan Masallaci a garin Malumfashi ta Jihar Katsina, ba makawa hakan ya nuna cewa, kamar an yi gaggawa kan ga murnar samun nasara ta yakin da ofishin Nuhu ke kan yi, da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga Daji duk da kuwa nasarar kame da kuma kashe wasu kasurguman ‘yan ta’adda da ofishinsa ya yi.
Kazalika, irin wannan salon ikirarin samun nasara a yakin da ‘yan ta’adda ne, Gwamnatin da ta shude ta rinka shelanata cewa, ta samu, amma a zari, batun akwai lauje a cikin nadi.
Domin kuwa, kusan shekaru takwas na Gwamnatin da ta gabata ta yi, kalubalen rashin tsaro ya jefa rayuwarsu, a cikin tasku, duba da yadda ‘yan tayar da kayan baya a kasar suka kusan durkusar da bangaren tsaron kasar, ta hanyar aikata ayyukansu na ta’addacin wanda lamarin ya kai ga har an nuna bukatar a yi wa fannin tsaron garanbawul.
Bugu da kari, ‘yan Nijeriya da dama,, sun ta yin kiraye-kirayen da a dauki mataki kan kalubalen rashin tsaro da ke addabar kasar a zahirance, ba wai kawai yin bayanai, da fatar biki da hukumomin tsaron kasar ke yi na cewa, sun kurmushe kaifin ‘yan ta’addar Kungiyar Boko Haram.
Hakazalika, a tsakanin wadannan watannin, manyan hukumomin tsaro na kasa sun ta yin bayanan zaurance domin nunawa ‘yan kasa tamkar komai na tafiya daidai, bayan alhali a bayan fage, ‘yan ta’adda na ta kai komon, yunkurin durkusar da kasa.
Har zuwa yanzu, ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin kwankwaton ikirarin da hukumomin tsaron kasar ke yi na murkushe kaifin ‘yan Boko Haram inda kuma a zahirance, ake ganin ‘yan gudun hijira a yankin Arewa Maso Gabas ke kara kwarara zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira da ke a yankin domin tsira da rayuwarsu.
A gefe daya kuma, manyan hanyoyin kasar sun koma tamar tarkon mutuwa ga matafiya inda ake tare su, a wasu yankuna, a hall aka su.
Masu garkuwa da mutane da sauransu, na ci gaba hana ‘yan Nijeriya sakat saboda ayyukansu da suke ci gaba da gudanarwa.
An dai nada Nuhu Ribadu a mukamin mai bai wa shugaban kasa shawara ne, bisa la’akari da nasarorin da ya samar, a lokacin da ya kasance shi ne shugaba na farko, na hukumar EFCC.
Nuhu tsohon Dansanda ne, wanda ya yi ritaya, a matsayin mataikin Sifeta Janar na ‘Yan Sanda.
Amma idan har zamu yiwa hukumomin tsaron adalaci, za mu iya cewa sun yi kokar wajen kashe ‘yanbindiga da dakile hare-haren ‘yan ta’adda a jihohohi kamar Zamfara, Katsina, Kaduna da Sokoto.
Sai dai, bisa maganar gaskiya, har yanzu za a iya cewa, akwai sauran gagarumin jan aiki, a gaba, game da magance matsalolin rashin tsaro a kasa.
Kalubalen rashin tsaro da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da fuskanta matsala ce da ke bukatar yin tunani mai zurfi da bunkasa salon dabarun yaki tare da daukar kwararan matakan da suka kamata, domin a kawo karshenta.
Kamata ya a ce, ofishin Nuhu Ribadu ya zama tamkar cibiyar da za a zauna a wasa kwakwalwar yin nazarin tsara yadda za a tunkari kalubalen rashin tsaron musamman duba da cewa, zuwa kai farmaki fagen daga ba hurumin sa ba ne.
Malam Nuhu Ribadu na da bukatar samun kwararru da za su taimaka masa da kuma shi kan shi tsarin tsaron kasa.
Bugu da kari, batun na samun nasara a yakar ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga, ba shi ne abin da a yanzu ‘yan kasa ke bukatar ji ba, domin a namu ra’ayin abin da suke bukata daga gun hukumomin tsaron shi ne, kara jajircewarsu wajen samar da dawamamen zaman lafiya a kasa.
Muna kira ga Malam Nuhu Ribadu da ya yi amfani da karfin ofishinsa wajen kara matsawa dakarun soji da ke a fagen daga na su kara kwazo kan yakin da suke ci gaba da yi da ‘yan ta’adda da kuma ‘yan bindiga.
A namu ra’ayin, nuna ganin kamar an yi riga Malam Masallaci kan batun cewa, an samu nasara kan yakar ‘yan tayar da kayar baya a kasar nan, musamman duba da cewa, har yanzu ‘yan Nijeriya na ci gaba da zama a cikin fargabar hare-haren’yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda.
Kazalika, duba da cewa, masallata a Masallatai na gudanar da ibada a cikin jimanin tsoro, wannan babban abin nuna damuwar ne bayan cewar, nauyi ne a kan jami’an tsaro su tabbatar da suna kare rayuka da dukokiyoyin ‘yan kasar .
Rashin imanin da ya aku a jihar Katsina da kuma a yankin Yelwata abune da ya nuna irin gazawar da ake da ita, bangaren samun bayanan sirri. A yayin da muke taya Fadar Shugaban kasa murnat samun wannan nasarar ,amma muna ganin har yanzu akwai sauran jan aiki a gaba kan batun kalubalen rashin tsaro a kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp ShareTweetSendShare Previous Post Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah Related Ra'ayinmu Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya 1 month agoকীওয়ার্ড: kalubalen rashin tsaro hukumomin tsaron hukumomin tsaro yan ta adda da samun nasara yan Nijeriya tsaron kasa yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
Sai dai don neman cimma burinta na “sake mayar da kasar Amurka zakaran gwajin dafi”, kasar Amurka ta sha daukar matakai na dakile ci gaban kasar Sin, ciki har da katse huldar tattalin arziki da ita da ma sanya takunkumai ga kamfanoninta masu ci gaban kimiyya da sauransu, duk da hakan, kasar Sin ta kiyaye bunkasar tattalin arzikinta yadda ya kamata, har ma karuwar tattalin arzikinta ta kai kaso 5.2% a cikin watanni tara na farkon bana, lamarin da ya shaida inganci da juriya na tattalin arzikin kasar. A kwanan nan, kasar Sin ta zartas da shawarwarin da aka gabatar game da tsara shirin raya tattalin arziki da zaman al’umma cikin shekaru biyar masu zuwa, kuma bisa ga shawarwarin, za a tsara shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15 na kasar. Cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, kasar Sin ta yi ta kokarin aiwatar da shirye-shiryen ba tare da kasala ba, ba don neman kalubalantar wata ko maye gurbinta ba, amma don mai da hankali a kan raya kanta da kuma bayar da damammaki na samun ci gaba ga sauran kasashen duniya.
Ganawar da aka yi a wannan karo ta kasance ta farko a tsakanin shugabannin kasashen biyu tun bayan da shugaba Trump ya sake hawa karagar mulkin kasar Amurka. Kafin wannan kuma, shugabannin biyu sun taba tattaunawa da juna ta wayar tarho har sau uku, don nuna alkiblar bunkasar huldar kasashensu. Tun bayan watan Mayun da ya gabata, bisa daidaiton da shugabannin biyu suka cimma, tawagogin kasashen biyu sun gudanar da shawarwarin tattalin arziki da cinikayya har sau biyar. A sabon zagayen shawarwarin da aka gudanar a baya bayan nan a birnin Kuala Lumpur, sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan tattalin arziki da ciniki da ke janyo hankulansu duka, tare da cimma matsaya daya a kan matakan da za a dauka. Lallai ta hanyar yin shawarwari da juna cikin daidaito, sassan biyu sun kai ga karfafa fahimtar juna da amincewa da juna, hakan kuma ya shaida cewa, yin shawarwari da juna ya fi yin gaba da juna, kuma Sin da Amurka suna iya raya kansu tare da tabbatar da ci gabansu na bai daya.
Kasancewarsu kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a duniya, alhakin da ke rataya a wuyan Sin da Amurka ne su gano hanyar da ta dace ta cudanya da juna. Kasashen biyu za su iya karfafa ginshikin huldarsu da samar da kyakkyawan yanayi na bunkasa kansu, tare da samar da karin tabbas da kwarin gwiwa ga duniya, muddin sun tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma suka yi hangen nesa tare da nacewa ga yin shawarwari da juna wajen daidaita sabaninsu, da kuma inganta hadin gwiwarsu da mu’amala da juna a kai a kai.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA