Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@19:35:54 GMT

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025

Published: 18th, September 2025 GMT

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawa Na 2025

Hukumar shirya jarabawar ta kasa NECO ta fitar da jarabawar SSCE dalibai dubu 818, 492 suka sami kiridit 5 zuwa sama da suka hada darasin Ingilishi da Lissafi.

 

Adadin bisa ga sakamakon ya nuna dalibai kashi sittin da biyu sun smai nasara.

 

Magatakardar NECO kuma Babban Jami’in Hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a lokacin da yake fitar da sakamakon jarabawar SSCE na shekarar 2025 a hedkwatar NECO da ke Minna babban birnin Jihar Neja.

 

Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ya bayyana cewa adadin dalibai miliyan daya da dubu dari da arba’in da hudu da dubu dari hudu da casa’in da shida da ke wakiltar maki tamanin da hudu da suka zana jarrabawar sun samu kiridit 5 ko sama da haka ba tare da la’akari da harshen Ingilishi da lissafi ba.

 

A cewar Farfesa Danteni “. A yayin gudanar da jarrabawar kammala sakandare ta shekarar 2025, (SSCE), an gano makarantu talatin da takwas suna yin magudin zabe) a jihohi talatin, yana mai jaddada cewa, za a gayyace su zuwa majalisar domin tattaunawa, bayan haka za a sanya takunkumin da ya dace.

 

Shugaban Hukumar NECO ya yi nuni da cewa an ba manya jami’ai Tara, Uku a Kogi, Daya a Niger, Uku a F.C.T, Daya a Kano da Daya a Jihohin Osun takardar gargadi saboda rashin kulawar da ake yi, wanda ya sa aka samu makara, rashin da’a, cin zarafi, da rashin biyayya.

 

Ya ce a lokacin Jarrabawar an samu rikicin kabilanci wanda ya haifar da bullar takardun jarrabawar a Jihar Adamawa daga ranar 7 zuwa 25 ga watan Yulin 2025 da ya shafi makarantu Takwas (8), inda ya ce jimillar darussa goma sha uku da takardu ashirin da tara (29) ne wannan lamarin ya shafa, sannan kuma dalibai dari biyar da casa’in da tara ne abin ya shafa.

 

NECO ta fara tattaunawa da jihar Adamawa da nufin gudanar da jarrabawar makarantun da abin ya shafa, inda ya nuna cewa ba za a iya fitar da sakamakon makarantun takwas a yanzu ba.” Inji magatakardan NECO.

 

Farfesa Dantani Wushishi ya bayyana cewa an fitar da sakamakon jarrabawar cikin gida na SSCE kwanaki hamsin da hudu bayan rubuta na karshe a watan Agusta, 2025, wanda ke nuni da cewa an kammala dukkan matakan da suka kai ga samun nasarar fitar da sakamakon cikin gida na 2025 SSCE.

 

Ya kara da cewa, fitar da sakamakon na cikin 2025 na SSCE cikin sauki, shaida ne na ma’aikatan Hukumar Jarrabawar bisa kwarewa, da’a da kuma ci gaba da neman nagartarsu, da sanin ya kamata, da kula da inganci, da jajircewa wajen bin ka’idojin da’a, sun tabbatar da cewa NECO ta samar da sakamakon da ya dace kuma dalibai, cibiyoyi da sauran jama’a suka amince da su.

 

 

Farfesa Dantani ya bayyana matukar godiya ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinuba bisa jajircewarsa wajen ganin an inganta ilimi ya samar da kyakkyawan yanayi ga hukumar NECO ta samu ci gaba, ya kuma yabawa ministan ilimi Dr Maruf Tunji Alyssa da karamin ministan ilimi Farfesa Suwaiba Said Ahmad bisa goyon baya da fahimtarsu.

 

COV ALIYU LAWAL.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: fitar da sakamakon Farfesa Dantani

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma