Aminiya:
2025-11-02@12:29:46 GMT

An yi kiciɓus da gawar ’yar shekara 14 a cikin gida a Kano

Published: 26th, August 2025 GMT

An yi kiciɓus da gawar wata budurwa mai shekaru 14 a cikin gidansu da ke unguwar Dandinshe a Ƙaramar Hukumar Dala da ke Jihar Kano.

Lamarin dai ya ɗugunzuma mazauna unguwar yayin da Aminiya ta riski iyaye, ’yan uwa da kuma maƙwabta cikin alhini a yayin ziyarar da ta kai har gida.

Hisbah ta haramta al’adun gargajiya yayin bukukuwan aure a Bauchi Trump ya yi barazanar korar Gwamnar Babban Bankin Amurka

Bayanai sun ce an yi arba da gawar Fatima Sulaiman rataye a jikin wata taga a cikin gidansu, lamarin da ya jefa shakku da ayoyin tambaya kan musabbabin mutuwarta.

Aminiya ta zanta da mahaifiyar marigayiyar, Malama Madina Inuwa Makwalla, wadda ta bayyana ganawa ta ƙarshe da ta yi da ’yarta.

“A ranar Asabar da yamma, muna shirin kai ziyara asibiti domin duba wani ɗan uwanmu.

“Da muka shirya tafiya, sai Fatima ta ce za ta shiga bandaki sannan ta biyo mu. Ashe ban sani ba, wannan ne karo na ƙarshe da zan gana da ita,” a cewar Madina tana faɗa cikin hawaye.

Mahaifiyar ta bayyana cewa har suka dawo daga asibiti Fatima ba ta biyo su ba, inda suka tarar da ƙofar gidan an kulle ta daga ciki, kuma duk wani yunƙurin buɗewa da suka yi da safayar makullin da ke hannunsu ya ci tura.

A wannan lokacin ne mahaifinta, Malam Sulaiman, wanda ya dawo daga kasuwa, ya haura ta katanga ya shiga gida, inda ya yi arba da abin da ba zai taɓa mantawa a rayuwarsa ba kamar yadda Malama Madina ta bayyana.

“Ya tarar da ɗiyarmu a rataye, babu rai. Ya yi matuƙar firgita, nan da nan ya kira ni, wanda ihun da na yi ya ankarar da maƙwabta suka yi ta taruwa,” in ji Malama Madina.

Mazauna unguwar da suka yi dandazon ganewa idanunsu wannan abun al’ajabi, sun bayyana shakku kan lamarin da cewa da yiwuwar akwai hannun wani, saboda alamu sun nuna an karya wuyanta kafin a rataye ta.

Mahaifin marigayiyar ya tabbatar cewa nan take suka sanar da ’yan sanda, waɗanda suka iso wurin, suka ɗauki gawar zuwa Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhammad, inda likitoci suka tabbatar da cewa rai ya yi mata halinsa tun kafin su kawo ta.

A cewarsa, “ba mu san wanda zai aikata wannan mummunan aiki ba. Amma muna kira ga hukumomin tsaro da su binciki lamarin sosai domin a gano masu hannu a ciki.

“Mun bar wa Allah wannan lamari. Muna roƙonSa Ya tona asirin duk wanda ya aikata wannan laifi. Allah Ya sa Aljannah ce makomarta.”

Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa sun soma cikakken bincike domin gano haƙiƙanin abinda ya faru domin tabbatar da adalci.

Maƙwabta da suka zanta da wakilinmu sun bayyana Fatima a matsayin yarinya mai ladabi, biyayya da girmama kowa.

“An santa da mutunci da zaman lafiya da kowa a unguwa. Wannan mutuwa ta girgiza mu gaba ɗaya,” in ji wani maƙwabci.

Tuni dai an binne gawar Fatima bisa koyarwar addinin Islama, inda ɗaruruwan jama’a suka halarci jana’izarta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: budurwa Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Umara Zulum ya sanar da fara fitar da kayayyakin robobi zuwa ƙasashen duniya wanda hakan ke nuna wani gagarumin ci gaba a wani ɓangare na ƙoƙarin farfaɗo da tattalin arzikin Jihar.

Gwamnan ya jaddada cewa, wannan matakin wani ɓangare ne na babbar ajanda na bunƙasa masana’antu da kuma kawar da dogaro da jihar kan yi na kason da gwamnatin tarayya ke bayarwa duk wata.

Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti

Zulum ya sanar da hakan ne a ranar Alhamis yayin rangadin duba masana’antar robobi ta Borno da ke cikin yankin masana’antu na Maiduguri.

“Ina farin cikin lura cewa mutanen Jihar Borno ba za su sake sayen kayan robobi daga wasu wurare ba, kun ga an sayar da kayayyakin ga ƙasashen maƙwabta da sauran jihohi a cikin Najeriya.”

“Za mu zuba jari sosai a masana’antunmu, don haka nan gaba kaɗan, gwamnatin Jihar Borno ba za ta sake dogara da asusun tarayya ba don ayyukanta na yau da kullum,” in ji Zulum.

Gwamnan ya bayyana cewa masana’antar ta fara fitar da kayayyakinta ga ƙasashen waje, tare da jigilar kayayyakin filastik da aka gama zuwa ƙasashe maƙwabta kamar Chadi da Jamhuriyar Kamaru.

Zulum ya lura cewa an fara gina cibiyar ne a lokacin gwamnatin tsohon Gwamna Kashim Shettima, amma an farfaɗo da ita a matsayin wani ɓangare na shirin murmurewa da ci gaban gwamnatinsa.

Wasu daga cikin kayan robobin

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum