Aminiya:
2025-09-17@20:28:12 GMT

Ambaliya: An gano gawar ’yar shekara 3 da ruwa ya tafi da ita a Zariya

Published: 14th, September 2025 GMT

An gano gawar Haneefa, yarinya ’yar shekara uku da ruwa ya tafi da ita lokacin da yayarta Fatima, ke goye da ita yayin ambaliyar da ta rutsa da su a Tudun Jukun da ke Zariya, a Jihar Kaduna.

An tsinci gawar ne bayan kwanaki shida da aka kwashe ana nemanta, a gangaren ƙasan Kilaco, unguwar Gyallesu, da misalin ƙarfe 11 na safiyar ranar Lahadi.

Ambaliya: NEDC ta raba wa mutum 2,200 kayan agaji a Yobe Likitoci sun janye yajin aikin da suka fara bayan kwana biyu

Babban jami’in ƙungiyar Red Cross a Zariya, Abdulmumin Adamu ne, ya tabbatar da gano gawar, inda ya ce hakan ya kawo ƙarshen binciken neman mutanen da ruwa ya tafi da su.

A ranar 8 ga watan Satumba, ambaliyar ruwa a Tudun Jukun, ta yi sanadin mutuwar ɗalibai biyu, Fatima Sani Danmarke da Yusuf Surajo (wanda aka fi sani da Abba).

A wannan lokacin ne kuma ruwa ya tafi da Fatima tare da ’yar uwarta Haneefa wadda ta ke goye a bayanta.

Kakan yarinyar, Malam Suleiman, ya ce an kira shi tare da shaida masa cewa wata bishiya ce ta riƙe gawar yarinyar a bayan Gyallesu.

Ya ce “A yau Lahadi da safe aka kira ni aka shaida min cewa an gano gawar Haneefa.

“Waɗanda suka gano ta sun ce wata bishiya ce ta tare gawar a can bayan Gyallesu Zariya.

“Don haka nan da nan muka yi mata jana’iza daga bisani kuma aka yi mata sutura aka binne ta,” in ji shi.

An yi wa Haneefa sutura tare da binne ta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Gawa yarinya Zariya ruwa ya tafi da

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

 

Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.

 

A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
  • An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
  • Ambaliya ta lalata gidaje da gonaki a Kaduna