Bikin Easter : Paparoma Francis ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza
Published: 21st, April 2025 GMT
Shugaban mabiya darikar Katolika na duniya Fafaroma Francis, ya yi kira da a tsagaita wuta a Gaza.
A cikin sakonsa na bikin Easter, Paparoma ya yi tir da halin da ake ciki na jin kai a Gaza tare da yin kira da a tsagaita wuta.
Paparoma Francis ya halarci bukukuwan Ista a wannan Lahadi, inda ya yi tir da halin da ake ciki na jin kai mai daukan hankali a Gaza.
“Ina kira ga bagarorin da su tsagaita wuta, a saki wadanda aka yi garkuwa da su, a kuma kai kayan agaji ga al’ummar falasdinu da kuma fatan samun zaman lafiya a nan gaba,” in ji shi a cikin sakonsa, wanda wani na hanun damansa ya karanto daga cocin St. Peter’s Basilica dake binrin Rome.
Jawabin nasa wani bangare ne na bikin Easter kamar yakke ake a ko wacce shekara, saidai fafaroman bai samu karanto jawabinba sabo lalurar ta rashin lafiya da yake fama da ita.
Mabiya addinin Kirisita a fadin duniya kan gudanar da bukukuwan Easter duk shekara domin tunawa da gicciyewa da kuma tashin Yesu Almasihu daga cikin matattu.
Bikin dai a kan fara shi ne tun daga dare irin na Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a a kuma kammala a ranar Litinin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
A yau Alhamis ne aka bude bikin baje kolin hada-hadar tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan, taron dake kara jaddada himmar kasar Sin ta fuskar karfafa alaka da nahiyar Afirka, nahiyar dake da mafiya yawan kasashe masu tasowa a duniya baki daya.
Kusan kamfanonin Sin da na kasashen Afirka 4,700, da sama da mahalarta 30,000 ne za su halarci bikin na kwanaki hudu, wanda aka yiwa taken “Sin da Afirka: Tunkarar zamanantarwa tare.” Rahotanni daga mashirya bikin na cewa, kwarya-kwaryar darajar ayyukan hadin gwiwa da aka amincewa sun haura dalar Amurka biliyan 11.
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin bude baje kolin, inda kuma ya yi amannar cewa taron zai samar da karin damammaki ga hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da haifar da kyakkyawan sakamako.
Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya kara da cewa, duk irin sauyin da aka samu a fannin cudanyar sassan kasa da kasa, Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da nahiyar Afirka, za ta samar da kakkarfan tallafi ga ayyukan zamanantar da nahiyar, da kasancewa kawa ta gari, kuma sahihiyar ‘yar uwa ga Afirka kan hanyar nahiyar ta samun ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp