HausaTv:
2025-05-21@21:23:51 GMT

Kasar Pakistan Ta Kara Jaddada Dokar Rashin Amincewa Da HKI A Matsayi Kasa

Published: 17th, April 2025 GMT

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Pakisatan ta kara jaddada matsayinta na rashin amince da HKI a matsayin kasa tana kuma goyon bayan Falasdinawa a gwagwarmayan da suke yi na kwatar yencinsu da kuma kasarsu daga hannun HKI da kuma kasashen yamma musamman Amurka masu goya mata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran wannan sanarwan tazo ne bayan da hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD ta samar da wani kuduri dangane da rikicin da ke faruwa a gabas ta tsakiya.

  A dai-dai lokacinda aka kara yawan tashe-tashen hankula a kasar Falasdinu da aka mamaye tsakanin HKI da kuma Falasdinawa masu gwagwarmaya. Kungiyar kasashe masu musulmi mafi rinjaye wato OIC ta yanke  shawara kan cewa bai kamata kasashen su samar da huldar Diblomasiyya da HKI ba.  Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Pakisatn ta bayyana cewa, kafafen yada labarai da dama sun watsa labaran cewa kasar ta Canza matsayinta dangane da kudurin hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD dangane da rikicin nag abas ta tsakiya, ta kuma kara da cewa wannan labarin ba gaskiya bane. Saboda kasar Pakistan tana tare da kungiyar OIC dangane da goyon bayan al-ummar Falasdinu. Don haka Pakisatan bata amincea da samuwar HKI ba. Har’ila yau majalisar kasa ta kasar Pakisatn ta amince da babban rinjaye ko kuma gaba dayan yan majalisar da rashin amincea da HKI da kuma goyon bayan Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci

Babban Mufti na kasar Oman ya bayyana cewa: Matakin taron kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ya fi kankara sanyi da rashin muhimmanci

Babban Mufti na masarautar Oman, Sheikh Ahmed bin Hamad Al-Khalili, ya jaddada yabonsa ga fitaccen matsayi na kasar Yemen da kuma matsin lamba da dakarun kasar Yemen suke yi na kai kayan agaji a zirin Gaza. A gefe guda kuma, ya nuna rashin jin dadinsa da raunin kudirin taron kasashen Larabawa kan daukan matakan matsin lamba kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila da take aiwatar da kashe-kashen gilla kan al’ummar Falasdinu.

A wani rubutu da ya yi a dandalin X, Al-Khalili ya bayyana godiyarsa ga jaruman kasar Yemen da kuma kasashen da suka bayar da gudumawa wajen matsin lamba don saukaka shigar da kayan agaji Gaza, yana mai cewa, “Ya gode wa Allah da shigar da wasu agajin da aka yi a Gaza,” yana mai jaddada bukatar ci gaba da daukan matakan matsin lamba na kasa da kasa wajen bude mashigar agaji gaba daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Babban Muftin Oman Ya Yi Suka Kan Taron Kungiyar Larabawa Saboda Rashin Saboda Rashin Ba Wa Gaza Muhimmanci
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Jaddada Shirinta Na Yaki Da  Matsalar Tsaro 
  • Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 
  • Ana Kara Samun Karuwar Sojojin HKI Da Suke Kashe Kansu
  • Kungiyar Hizbullah Ta ce Marigayi Shahid Ra’isi Ya Kasance Mai Taimakawa Kasar Lebanon Da Kuma Falasdinawa Ne
  • Iran Ta Kira Jakadan Burtaniya A Tehran Saboda Tuhumar Da Akewa Iran Da Leken Asiri A London
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: FCT Ta Lallasa Borno Da Ci 4-1 A Wasan Farko
  • Fahimtar Hakikanin kasar Sin
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran