Aminiya:
2025-11-03@03:44:36 GMT

An Kashe Shanu 36, an ba 42 guba a Filato

Published: 17th, April 2025 GMT

Shanu 36 sun mutu baya ga wasu 42 da ake zargin an ba su guba guba a kusa da yankin mahaɗar Tafi Gana a Ƙaramar Hukumar Bassa ta Jihar Filato.

Shugaban Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) a Karamar Hukumar Bassa, Ya’u Idris, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yamma lokacin da shanun ke kiwo a yankin.

Ya’u ya ƙara da cewa an sanya guba ne a cikin gauta, waɗanda aka warwatsa a kewayen wurin kiwon kuma shanun suka ci.

Ya ci gaba da cewa sun kai rahoton lamarin ga dukkan hukumomin tsaro ciki har da Hukumar DSS, da ’yan sanda, ya kuma  Babban Kwamandan Rundunar ta kuma din ya ziyarci wurin da abin ya faru.

Wannan lamarin ya faru ne kwanaki biyu kacal bayan wani mummunan hari a kauyen Zikke, a cikin wannan ƙaramar hukumar ta Bassa, inda aka kashe mutane 52 tare da jikkata wasu da dama. An kuma kona gidaje da dama a harin.

Mazauna yankin da aka kai harin sun zargi makiyaya da hannu a kashe-kashen da aka yi a ranar Litinin, zargin da makiyayan suka musanta.

Kakakin rundunar tsaro ta Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai amsa saƙon da wakilinmu ya aike masa ba game da lamarin a lokacin da ake rubuta wannan rahoto.

An haramta kiwon dare da hawa babur

A sakamakon ƙaruwar rashin tsaro, Gwamna Caleb Mutfwang a ranar Laraba ya haramta kiwon dabbobi da daddare, da kuma jigilar shanu da hawa babura bayan ƙarfe 7 na yamma. Wannan matakin na daga cikin hanyoyin da gwamnatin jihar ta ɗauka domin hana ci gaba da samun sabani tsakanin makiyaya da manoma.

Gwamnan, a cikin wani jawabi da ya yi wa al’ummar jihar a ranar Laraba, ya bayyana cewa a makon da ya gabata, an kai hari kauyen Zikke inda aka kashe mutane da dama.

Sai dai, wannan dokar ta haifar da ce-ce-ku-ce, musamman ma daga direbobin manyan motocin da ke Jos, waɗanda suka bayyana haramcin jigilar shanu bayan karfe 7 na yamma a matsayin wanda ya ci karo da wata doka da ta riga ta hana zirga-zirgar manyan motoci tsakanin karfe 6 na safe zuwa 9 na yamma. Sun kuma roƙi gwamnatin da ta sake duba wannan doka.

Haka kuma, kungiyar MACBAN ta nuna damuwarta game da wannan doka, inda ta bayyana cewa lokacin da aka ƙayyade zai iya shafar rayuwar makiyaya, musamman wadanda za su iya kasancewa tare da shanunsu a kasuwanni bayan karfe 7 na yamma.

Sun cewa suna goyon bayan dokar domin tabbatar da zaman lafiya, amma suna roƙo gwamnan da ya ɗaga lokacin zuwa karfe 8 na dare domin mutanensu su samu damar komawa gida lafiya.

Laifin gwamnatocin baya ne — Gadgi

A nasa ɓangaren, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Pankshin Kanke da Kanam a Jihar Filato, Yusuf Adamu Gagdi, ya bayyana cewa abin takaici ne yadda yankunan da suka yi fice wajen noma a Bokkos, Bassa, Wase, da Mangu suka zama filin daga.

Ya zargi gazawar gwamnatocin baya wajen ba kama shugabannin hukumomin tsaro da laifin  gazawarsu wajen samar da tsaro a yankunansu da ta haifar da karuwar matsalar tsaro a kasar.

Gadgi ya kuma alaƙanta ƙaruwar hare-hare a Filato da tserewar da ’yan bindiga ke yi daga jihohi Zamfara da Sakkwato zuwa dajin Filato sakamakon ragargazarsu da sojoji suka tsananta.

Za mu dawo da zaman lafiya — ’yan sanda

Mataimakin Sufeto Janar na ’Yan Sanda (DIG) Kwazhi Bzigu Dali ya ziyarci yankunan da aka kai hari domin tantance halin da ake ciki, inda ya gudanar da sintiri ta sama da ƙasa tare da ganawa da shugabannin ƙananan hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki.

Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin da cewa Sufeto-Janar na ’Yan Sanda ya ƙudiri aniyar dawo da zaman lafiya, inda ya sanar da tura karin jami’an tsaro da kayan aiki.

Dattawan Arewa sun fusata

Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kakkausar suka ga kashe-kashen da ake yi a Filato, inda ta bayyana su a matsayin abin kunya ga ƙasa.

Sun soki rashin ɗaukar mataki da Gwamnatin Tarayya ke yi, suna masu kira da a tura jami’an tsaro da kayan aiki nan take tare da tabbatar da an yi adalci.

Haka kuma, Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ta nuna baƙin cikinta game da sake ɓarkewar rikicin a Filato, inda ta yi kira ga shugabannin al’umma da na addini da su tallafa wa Gwamna Mutfwang wajen kwantar da hankula da kuma gina zaman lafiya mai ɗorewa.

Gwamnatin Tarayya ta sake nanata ƙudirinta na kawo ƙarshen rashin tsaro a faɗin ƙasar, inda ta bayyana ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsaron kasa.

Tsohon ɗan takarar Shugaban Ƙasa na Jam’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi kira ga gwamnatin da ta daina magana ta fatar baki kawai, ta ɗauki matakai na zahiri don kare ’yan Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Makiyaya Mutfwang Tsaro zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan kalaman da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi game da Najeriya.

Kwankwaso, ya yi wannan magana ne bayan Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi game da zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.

Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya ce Najeriya ƙasa ce mai cikakken ’yanci, wadda ke fama da matsalar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar.

“Matsalar tsaron da muke fuskanta ba ta bambanta tsakanin addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji shi.

Ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta tallafa wa Najeriya da sabbin fasahohi domin yaƙar matsalar tsaro maimakon yin kalaman da za su iya raba kan ’yan ƙasa.

“Amurka ya kamata ta taimaka wa hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance matsalolin tsaro, maimakon yin barazanar da za ta ƙara raba ƙasar,” in ji Kwankwaso.

Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Najeriya da ta naɗa jakadu na musamman domin inganta hulɗar diflomasiyya da Amurka da kare muradun ƙasar a matakin duniya.

Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su zauna lafiya, inda ya bayyana cewa wannan lokaci ne da ya dace a fifita haɗin kan ƙasa ba abin da ke raba ta ba.

“Wannan lokaci ne da ya kamata mu mayar da hankali kan abin da zai haɗa kanmu ba wanda zai raba mu ba. Allah Ya albarkaci Najeriya,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa