Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025
Published: 6th, April 2025 GMT
A yayin hirar Abdullahi Shuaibu ya ce “Ni dai suna na Abdullahi Shuaibu, amma al’uma na kirana da Karkuzu, ko kuma Abdullahi Kano, yanzu shekaru 43 kenan ina wannan harka ta fina finan Hausa, amma yanzu wasu lokutan sai in kwana ba ni da abin da za a ci a gida na, kuma wani abin tausayi, ni Karkuzu a yanzu zancen da na ke, wannan gida da nake ciki an sa shi a kasuwa, ba gida na ba ne, haya nake yi.
Ya ci gaba da cewa, yanzu a cikin wannan al’amari da na ke yi, in an ce na mallaki gida mai dimbin yawa, wadansu da za su ke kallo na sai su ce gaskiya ne, amma wallahi tallahi, daki daya bani da wani gida da za a kalla ace wannan mallakina ne, na rasa ido yanzu zancen da na ke mai kallo na ba na gani.
A kan batun ‘yan fim da za su iya taimaka masa, Karkuzu ya ce ba wai al’ummar Kano kawai ko al’ummar Jos, Kaduna ko na Legas ba, duk al’ummar duniyar nan ina bukatar a taimaka min, wannan gida yanzu da aka sa shi a kasuwa za a sayar, ba ni da kudi, bayan ba ni da kudi ba na gani, ba na zuwa ko’ina, ina da ‘ya’ya, maganar abinci kam ma babu, wannan shi ne zahirin gaskiya inji Karkuzu a hirar su da TRT Hausa na ranar 10 ga watan Agusta 2023.
A wancan lokacin sakamakon wannan neman taimako da ya yi, kyaftin din tawagar kwallon kafa ta Nijeriya Ahmed Musa ya gwangwaje Karkuzu da kyautar makudan kudade har Naira 5,000,000, sannan kuma ya ba da umarnin a nemo gida ya saya masa, wanda bai wuce naira miliyan hudu zuwa biyar ba, kuma haka aka yi, domin kuwa Ahmed Musa ya saya masa gida na N5,500,000 kafin rasuwarsa.
Karkuzu ya yi manyan fina-finai madu dimbin yawa da tasiri a masana’antar Kannywood, daga cikinsu akwai Gida Da Waje, Ga Duhu Ga Haske wanda su ka shirya da Jaruma Zainab Muhammad (Indomie), a tsawon shekaru fiye da 40 da ya shafe a masana’antar Kannywood ya yiwa da dama a cikin jarumai hanyar samun daukaka a masana’antar.
Tasirin marigayi Abdullahi Shuaibu Karkuzu ba boyayye ba ne a jahar Kano, Arewacin Nijeriya da ma kasar bakidaya, wata sanarwa da babban daraktan yada labarai na gwamnan jahar Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar 28 ga watan Maris wadda LEADERSHIP Hausa ta fassara ya nuna yadda gwamnan jahar Abba Kabir Yusuf ya yi ta’aziyar mutuwar Abdullahi Shuaibu Karkuzu.
Sanarwar ta ce: “Gwamna Yusuf Ya Yi Ta’aziya Ga Masana’antar Kannywood Da Iyalan Shahararren Jarumin Kannywood Karkuzu Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi alhinin rasuwar shahararren jarumin Kannywood, Abdullahi Shuaibu wanda aka fi sani da Karkuzu wanda ya rasu a kwanakin baya bayan doguwar jinya, Karkuzu ya rasu ya na da shekaru 94 a duniya.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a Kano ranar Juma’a, Gwamnan ya ce mutuwar babban rashi ne ga masana’antar Kannywood na wani wanda ya kira kwararren jarumi mai fikira, da ya jajirce wajen yin sana’ar tare da taimako wajen tasowar yan wasa da dama a masana’antar.
Ya ci gaba da cewa marigayin ya bar wani gibi da zai yi wuyar cikewa cikin sauki, a shekarun da ya kwashe a masana’antar, ya nuna kwarewa iri-iri da kuma kokarin kawo sauyi ta hanyar nishadantarwa da kuma fadakarwa.
A madadin gwamnati da jama’ar Jihar Kano, gwamnan ya na mika sakon ta’aziyya ga iyalan mamacin, ‘yan Kannywood da masana’antar fim.
Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya kyautata makwancinsa ya kuma baiwa ruhinsa dawwamammen aminci a cikin kabari, ya kuma roki Allah ya sa Aljanna Firdausi ce makomarshi.”
Wannan ya sa muka rubuta makalar “BA RABO DA GWANI BA” domin tunawa da wannan dattijo da ya shafe kusan rabin shekarun rayuwarshi domin ya nishadantar ya kuma fadakar da al’umma ta hanyar fina-finan Hausa, Karkuzu zai shafe tsawon lokaci ana tunawa da irin gudunmawar da bayar wajen kawo masana’antar Kannywood matsayin da ta ke a yanzu.
Hakazalika masu sha’awar kallon fina finan Hausa zasu dade su na kallon marigayin a matsayin wani mutum da ya nishadantar da kuruciyarsu ya kuma fadakar da tsufansu ta hanyar fina finanshi, sannan kuma matasa a masana’antar Kannywood za su tuna Karkuzu a matsayin wani jigo da su ka kwaikwayi ayyukanshi kuma sukayi amfanin da shawarwarinshi wajen samun daukaka a masana’antar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: gwani a masana antar Kannywood
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.
Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.
Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.
Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.
“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.
Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.
Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.
“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.
Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.
“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.