Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
Published: 21st, March 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan, a sakonsa na karshe ga Iraniyawa a shekara ta 1403 na kalandar Iraniyawa, ya bukaci mutanen kasar su hada kai don kaiwa ga manufofin kasar, wadanda suka hada da bunkasar tattalin arziki, da kauda tsadar rayuwa da kuma rashin bawa makiya damar cutar da kasar.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jawabinda na ‘Nuruz’ ko sabon shekara ta 1404 wanda ya shigo yau.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
Wani mutum ya mutu, wasu da dama kuma sun jikkata lokacin da wata tirela ta yi karo da wata mota ƙirar akori kura Mitsubishi Canter a Damagum da misalin ƙarfe 12:50 na tsakar dare a ranar Laraba.
Kamar yadda kakakin rundunar ‘Yan sanda Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkareem ya ce tirelar, mai lambar rajista MUS 791 XH, wacce Aliyu Muhammad, mai shekara 30, daga Azare, ƙaramar hukumar Katagum, Jihar Bauchi ke tuƙawa tana tafiya daga Damaturu zuwa Legas lokacin da motar ta kufcewa direban ta afka wa motar da ke gabanta.
Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris NgigeMotar, mai mutane 18 da ke ciki da lamba AA 641 PKM, wadda Usman Muhammad, mai shekara 40 daga ƙauyen Yaskawel ne ke tuƙa ta.
Mai magana da yawun rundunar ya ce, an tabbatar da mutuwar fasinja ɗaya, Ɗahiru Maikuɗi mai shekara 40, daga ƙauyen Yaskawel, a babban asibitin Damagum yayin da wasu da dama suka jikkata.
A cewar rundunar, an tura waɗanda abin ya shafa shida zuwa asibitin Koyarwa da ke Damaturu don ƙarin kula da lafiyar su.
Hatsarin ya haifar da zanga-zanga daga matasan Damagum waɗanda suka koka game da yawan haɗurra a kan babbar hanyar Damaturu zuuwa Potiskum, musamman kusa da Damagum inda ake harkokin kasuwanci da zirga-zirgar masu sufuri a ƙasa ke ƙaruwa musamman a ranakun Lahadi da Laraba.
Jami’an ‘yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zangar don hana cin zarafin da ake yi wa mutane.
Kwamishinan ‘yan sandan Jihar, Emmanuel Ado ya yi wa iyalan wanda ya rasu ta’azɗiyar rashin mamacin ya jajantawa waɗanda suka jikkata yayin wannan hatsari yana mai umurtar Jami’in ‘yan sandan yankin da ya yi aiki tare da ƙaramar hukumar kan matakan kariya na dogon lokaci.
Ya gargaɗi masu ababen hawa game da yin gudun wuce ƙima kuma ya yi kira da a bi ƙa’idodin zirga-zirga sosai, yana mai gargaɗin cewa, waɗanda suka karya doka za su fuskanci hukunci.
Kwamishinan ya kuma shawarci mazauna yankin da su guji yin harkokin kasuwanci kusa da babbar hanyar don rage ƙarin faruwar haɗurra.