Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
Published: 21st, March 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan, a sakonsa na karshe ga Iraniyawa a shekara ta 1403 na kalandar Iraniyawa, ya bukaci mutanen kasar su hada kai don kaiwa ga manufofin kasar, wadanda suka hada da bunkasar tattalin arziki, da kauda tsadar rayuwa da kuma rashin bawa makiya damar cutar da kasar.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jawabinda na ‘Nuruz’ ko sabon shekara ta 1404 wanda ya shigo yau.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Muscat Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Kama Hanyar Zuwa Birnin Domin Ci Gaba Da Tattaunawa Da Amurka
Ministan harkokin wajen Iran ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a yau domin gudanar da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba da Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya sanar da cewa: A yau ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya nufi birnin Muscat na kasar Oman a karkashin jagorancin tawagar diflomasiyya da fasaha don shiga zagaye na uku na shawarwarin da ba na kai tsaye ba da Amurka ta hanyar shiga tsakanin mahukuntan Oman.
Baqa’i ya bayyana cewa: Bangarorin biyu sun amince da gudanar da tarukan fasaha tare da halartar manyan jami’an shawarwari, yana mai bayanin cewa “bisa tsarin da Oman ta shirya da kuma hadin gwiwa tsakanin Iran da Amurka, za a gudanar da tarukan fasaha da shawarwari kai tsaye tsakanin ministan harkokin wajen Iran da wakilin shugaban Amurka na musamman a ranar Asabar.”
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Ci gaban da ake samu a shawarwarin yana bukatar daya bangare ya nuna kyakykyawar fahimta, da gaske, da kuma hakikanin gaskiya, yana mai jaddada cewa: Tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki ne bisa gogewar da ta gabata da kuma dabi’ar daya bangaren, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen cimma halaltacciyar hakki da muradun al’ummar Iran.