Aminiya:
2025-05-01@02:24:01 GMT

NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA, ta bayar da lasisin kafa sabbin matatun man fetur uku a wasu jihohin ƙasar uku.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X a ranar Asabar, wadda shugabanta, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.

Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol

NMDPRA ta ce ta bayar da lasisin gina sabbin matatun man ne a jihohin Abia da Delta da kuma Edo.

“Za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a Jihar Edo.

“Za kuma a buɗe Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a Jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a Jihar Abia.”

Hukumar ta ce sabbin matatun uku idan an kammala su gaba ɗaya za su iya tace ganga 140,000 na man fetur duk rana.

Bayanai daga hukumar ta NMDPRA sun nuna cewa Nijeriya na da matatun man fetur tara, ciki har da sabuwar matatar Dangote da ke birnin Legas.

Waɗannan matatu na tace ganga 974,500 a duk rana, yayin da Matatar Dangote kaɗai ke da ƙarfin tace ganga 650,000 a kowace rana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote NMDPRA

এছাড়াও পড়ুন:

Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya

Majalisar Shari’ar Musulunci ta Najeriya ta naɗa Sheikh Bashir Aliyu Umar a matsayin shugabanta bayan rasuwar Sheikh AbdulRasheed Hadiyyatullah.

Wata sanarwa da majalisar ta fitar a yau Laraba ta ce an amince da shuagabancin Dokta Bashir ne kai-tsaye saboda kasancewarsa mataimakin shugaba.

A ranar Litinin ne Sheikh Hadiyyatullah ya rasu yana da shekara 81 a Jihar Osun.

“Nan gaba za a sanar da mataimakin shugaban,” in ji sanarwar da Nafiu Baba Ahmed ya sanya wa hannu a matsayin sakataren majalisar.

Sheikh Bashir sanannen malami ne kuma shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Al-Furqan da ke Alu Avenue a Unguwar Nasarawa ta Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba