Aminiya:
2025-03-21@22:39:41 GMT

NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA, ta bayar da lasisin kafa sabbin matatun man fetur uku a wasu jihohin ƙasar uku.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X a ranar Asabar, wadda shugabanta, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.

Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol

NMDPRA ta ce ta bayar da lasisin gina sabbin matatun man ne a jihohin Abia da Delta da kuma Edo.

“Za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a Jihar Edo.

“Za kuma a buɗe Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a Jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a Jihar Abia.”

Hukumar ta ce sabbin matatun uku idan an kammala su gaba ɗaya za su iya tace ganga 140,000 na man fetur duk rana.

Bayanai daga hukumar ta NMDPRA sun nuna cewa Nijeriya na da matatun man fetur tara, ciki har da sabuwar matatar Dangote da ke birnin Legas.

Waɗannan matatu na tace ganga 974,500 a duk rana, yayin da Matatar Dangote kaɗai ke da ƙarfin tace ganga 650,000 a kowace rana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote NMDPRA

এছাড়াও পড়ুন:

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i

Sun kuma bayyana cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta manyan makarantun da ake da su na tarayya da kuma jihohi, ta hanyar samar da wadatattun kudade, inganta abubuwan more rayuwa da kuma tabbatar da ganin ma’aikatan jami’i’on, sun samu horo na musamman da suke bukata da kuma tallafa musu.

Wani mai ba da shawara a kan harkokin binciken ilimi a Jami’ar Abuja, Humphrey Ukeaja, ya gano wasu damammaki da kalubale iri-iri da aka samu kwanan nan.

Masanin ya yi nuni da cewa, rashin samun wadatattun kudade a fannin ilimi a Nijeriya, ya zama wani babban al’amari. “Idan kuna son yin wannan sauyi misali, mayar da jami’i’o’i zuwa na gwamnatin tarayya, har yanzu a kwai ayar tambaya, shin za ku inganta su ne kokuwa inganta kudaden da za a bai wa sabbin jami’o’in? Domin kuwa, wannan ba karamin kalubale ba ne. saboda haka, gwamnati tana da kyakkyawan kudiri ne na daukar cikakken nauyin wannan ilimi?”.

Canzawa tare da kara wasu makarantu ba tare da daukar cikakken nauyinsu ba, zai sa ba za su iya tsayawa da kafafunsa, wanda a karshe ko kadan ba za a samu abin da ake nema ba na biyan bukata, in ji shi.

Farfesa Ukeaja, na da ra’ayin cewa, kafa jami’o’in tarayya a wurare kamar Kachia, zai taimaka wajen inganta ilimi tare da rage tazarar da ke tsakanin birane da kauyuka ta fannin samar da ilimi. “Don haka, idan har za a samar da jami’o’i a wuraren da suka dace, babu shakka wannan zai zama wani babban ci gaba”, in ji shi.

Ya ba da shawarar cewa, ya kamata gwamnatin tarayya ta kara yawan kudade ga fannin ilimi tare da fadada hadin gwiwa da jami’o’i masu zaman kansu, domin inganta jami’o’in, bai wa malamai horo na musamman da sauran makamantansu.
Har ila yau, kungiyar daliban Nijeriya; sun yaba da matakin, amma kuma sun nuna damuwa a kan lamarin.

Jami’in hulda da jama’a na kungiyar dalibai ta kasa (NANS), Kwamared Samson Ajasa Adeyemi, ya bayyana jin dadinsa kan kokarin da gwamnatin tarayya ke yi na magance matsalolin ilimi a Nijeriya, musamman kan yadda take mayar da makarantun jihohi zuwa na tarayya.

Sai dai ya koka da cewa, daya daga cikin manyan kalubalen da ke fuskantar fannin na ilimi a Nijeriya, ya hada da rashin isasssun kudade.

Ajasa ya yi nuni da cewa, da dama daga cikin wadannan manyan makarantun gwamnati, sun dogara ne da kudaden basussuka wajen tafiyar da makarantun, sannan akwai bukatar aiwatar da gaskiya wajen aiwatar da kasafin kudin yadda ya kamata, domin tabbatar da ganin an yi amfani da wadannan kudade yadda ya dace.

A nasa bangaren, wani dan kishin kasa, Mista Tochukwu Osuagwu, ya bukaci gwamnati ta kara zuba hannun jari a jami’o’in da ake da su, domin inganta su yadda ya kamata.

“Me zai hana a mayar da hankali wajen inganta jami’o’in da ake da su a fadin wannan kasa baki-daya, ko shakka babu, Nijeriya za ta ci gaba idan muka riki junanmu da gaskiya.

“A bayyane yake cewa, jami’o’inmu na cikin wani mummunan yanayi, wanda ba haka ya kamata al’amarin ya kasance ba, kyautuwa ya yi a ce jami’o’inmu sun samu wadatattun kayan aiki da ci gaba kamar yadda ake gani a wasu sauran kasashe”, in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Xi Ya Bukaci A Bude Sabbin Hanyoyin Samun Ci Gaba Yayin Rangadinsa A Lardin Yunnan
  • Najeriya: Ana Fargabar Sake Tashin Farashin Fetur Bayan Dangote Ya Daina Sayar Da Mai A Naira
  • Amurka Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen Don Tallafawa HKI
  • Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira
  • Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira