“Wasu masu kiwon, suna zuwa shagunan sayar da magani ne su sayo su rika bai wa dabbobin da suka harbu da wata kwayar cuta, ba tare da yin la’akari kan adadin magungunan da ya kamata su ba su ba”, in ji Ngulukun.

Ana kuma bukatar masu kiwon su dakar da bai wa dabbonin nasu magunguna daidai da lokacin da misali, kajin gidan gona ke shirin fara yin kwai ko kuma lokacin da shanu ke shirin fara samar da madara, domin kare lafiyar mutane.

Sai dai, abin takaici shi ne, akasarin masu kiwon; ba sa kiyaye irin wadannan lokuta, wanda hakan ke shafar lafiyar mutanen da suka yi amfani da irin wadannan dabbobi.

Kazalika, yawan bai wa dabbobin magungunan barkatai don yakar wasu kwayoyin cutar da ta harbe su, na iya sanya wa ko da an bai wa dabbobin magungunan, su ki yin wani amfani a jikinsu.

Har ila yau, duk da cewa; an samar da dokoki a kan wannan matsala, sai dai, ana ci gaba da samun sakaci wajen tilasta kiyayewar yawan shayar da dabbobin magungunan barkatai, ba tare da masu kiwon sun samo shawarar Likitocin dabbobin ba.

A cewar wasu kwararru a fannin, wannan matsalar na jawo karuwar mutuwar dabbobi tare kuma da jawo asara ga masu kiwonsu.

A yanzu haka, saboda wannan batu na bai wa dabbobin magunguna, hakan ya jawo bijirewar da kwayar cutar ke yi na haifar da mutuwar dabbobi a duk shekara da yawansu ya kai kimanin miliyan 4.95, inda mafi akasari aka fi alakanta mutuwar tasu kai tsaye da kimanin miliyan 1.27, inda kwararrun suka yi gargadi da cewa, idan har ba a dauki matakan da suka dace ba, nan da 2050, adadin mutuwar dabbobin zai kara rubanya zuwa miliyan 10.

Bugu da kari, Nijeriya na daga cikin kasashen da ake fuskantar irin wannan matsala, inda aka alakanta mutuwar akalla duk shekara kimanin 263,400, sakamakon rashjin jin magani da kwayoyin cutar da ke harbin dabbobin ke yi.

Wani kwararre a bangaren kula da lafiyar dabbobi, Dakta Nafiu Lawal, ya shaida wa jaridar LEADERSHIP cewa, ba a mayar da hakankali wajen wayar da kan masu kiwon dabbobin kan wannan matsala.

Dakta Nafiu, ya shawarci masu kiwon dabbobin da su rika tuntubar kwararrun likitocin dabbobi, domin samun shawarwari kan irin magungunan da ya kamata su rika bai wa dabbobin nasu, bayan sun kamu da kwayoyin cututtuka.

Sama da shekaru takwas da suka gabata, Nijeriya ta samar da tsare-tsare na kasa guda biyu a bangaren kiwo, ciki har da yadda za a dakile wannan matsala.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fargaba bai wa dabbobin wannan matsala

এছাড়াও পড়ুন:

Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza

Mummunar yunwa a Gaza.. Wakilin gidan talabijin na Al-Alam ya bayyana cewa: Shi da iyalansa kwana biyu ba su ci abinci ba

Wakilin gidan talabijin na Al-Alam na kasar Iran ya ruwaito cewa: An samu barkewar yunwa mai tsanani a Gaza, inda ya tabbatar da cewa ya kwashe kwanaki biyu bai ci komai ba.

Basil Khairudden wakilin gidan talabijin na Al-Alam a Gaza, ya ce: “A ranar Juma’a, shi da iyalinsa da daukacin al’ummar Gaza ba su iya samun ko da biredi guda da za su ci ba, sakamakon yunwa da ake fama da ita a Gaza.”

Ya tabbatar da cewa a Gaza akwai mutanen da ba su ci abinci ko da sau daya a tsawon kwanaki uku. A ranar Juma’a mutanen Gaza sun yi ta yawo a kasuwanni, tituna, da unguwanni ba tare da samun kilo guda na gari ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola
  • An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar