Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya jaddada kudurin Najeriya na aiwatar da cikakken yarjejeniyar biyu da aka kulla tsakanin China Media Group da manyan gidajen watsa labarai na gwamnati a Najeriya – Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN) a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a Beijing.

 

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi Jakadan Sin a Najeriya, Mista Yu Dunhai, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa a yau alhamis. Ya ce, wadannan yarjejeniyoyi sun ƙudiri aniyar ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin watsa labarai da sadarwa, domin inganta dangantakar Najeriya da Sin.

 

Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun shafi musayar bayanai da fasahar zamani, wanda hakan zai inganta ƙwarewar gidajen watsa labaran Najeriya tare da ɗaukaka su zuwa matakin da ya dace da kyawawan ƙa’idojin duniya.

 

“Najeriya da Sin a matakin hulɗar diflomasiyya suna da ƙawance mai ƙarfi matuka. Wannan ya haifar da sanya hannu kan yarjejeniyar fahimta guda 10 a Beijing, kuma guda biyu daga cikinsu suna da nasaba da wannan ma’aikata. Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) ita ce cibiyar talabijin mafi girma a duk faɗin Afirka, tana da tashoshi sama da 100 da ke rufe dukkan yankuna tare da isa ga mutane sama da miliyan 200. Yana da matuƙar muhimmanci, kuma abin da NTA ke son cimmawa ta hanyar wannan haɗin gwiwa da Sin shi ne musayar labarai, fasaha, da bayanai wanda zai amfanar da ƙasashen biyu. Haka kuma, muna da irin wannan yarjejeniya da ɗaya daga cikin manyan gidajen rediyo a Afirka, wato Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN). Wadannan yarjejeniyoyi sun riga sun kammala, kuma Najeriya tana da niyyar cika nata ɓangaren,” in ji shi.

 

Ministan ya ce, bayar da sahihin bayani da labarai na gaskiya zai ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashe, don haka ya nemi haɗin gwiwa da Sin wajen yaƙi da labaran ƙarya, ɓata bayani da yada bayanai na bogi.

 

“Yada labaran ƙarya ƙalubale ne ga duniya baki ɗaya. Mun san cewa Sin tana ɗaukar wannan batu da muhimmanci sosai, haka kuma mu ma a Najeriya muna ɗaukar hakan da muhimmanci. Ba matsala ba ce da ke shafar Najeriya da Sin kaɗai; matsala ce ta duniya baki ɗaya, kuma muna son yin aiki tare da Sin don yaƙi da labaran ƙarya tare da inganta watsa labarai masu amfani da za su taimaka wajen bunƙasa al’umma,” in ji shi.

 

Idris ya bayyana wa Jakadan cewa, Najeriya na da ‘yancin watsa labarai a matsayin wani muhimmin bangare na manufofin gwamnatin Tinubu don ƙarfafa dimokuradiyya ta hanyar bayar da ingantattun bayanai.

 

“Kafafen watsa labarai a nan suna da ’yanci sosai. Tabbas, akwai wasu matsaloli a lokaci zuwa lokaci, wanda koyaushe muna aiki a kansu don ingantawa. Najeriya na da babbar ’yancin watsa labarai, kuma muna so mu ci gaba da hakan,” in ji shi.

 

Ministan ya kuma bukaci kamfanonin Sin su yi amfani da sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa domin zuba jari a tattalin arzikin Najeriya.

 

A nasa jawabin, Jakada Dunhai ya ce a matsayinsa na sabon jakadan Sin a Najeriya, zai yi duk mai yiwuwa don ƙara ƙarfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

 

Ya nuna goyon bayansa ga shirin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu, wanda ke da nufin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa don samar da ci gaba mai dorewa.

 

“A matsayina na sabon jakada, ina ganin kaina a matsayin mai sa’a saboda na zo ne a lokacin da Najeriya ke karkashin jagorancin Shugaba Tinubu, wanda ke da niyyar gina ƙasa mai ƙarfi. Haka nan, a karkashin jagorancin Shugaba Xi Jinping, Sin tana kan tafarkin sabunta ƙasa ta hanyar tsarin zamani na Sin,” in ji shi.

 

Jakadan ya tunatar da cewa a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a Beijing, Shugabannin kasashen biyu, Xi Jinping da Tinubu, sun amince da ɗaukaka dangantakar kasashen su zuwa babbar kawance ta fuskar diflomasiyya, wanda hakan zai buɗe sabon babi a dangantakar su.

 

Ya ce yana sa ran ganin yadda za a aiwatar da yarjejeniyoyin fahimta da aka kulla tsakanin NTA, FRCN da China Media Group, domin kafafen yada labarai suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen gina al’umma.

 

Jakadan ya bayyana jin daɗinsa cewa kafafen watsa labarai a Najeriya suna daidaito, gaskiya da adalci a labaran da suke watsawa, domin suna ƙoƙarin gabatar da cikakken bayani kan abubuwan da ke faruwa ga ‘yan Najeriya.

 

A bangaren zuba jari, Jakadan ya ce Shugaba Xi Jinping ya alkawarta dala biliyan 50 domin zuba jari a Afirka a cikin shekaru uku masu zuwa, a matsayin ci gaba ga yarjejeniyoyin fahimta guda goma da aka rattaba hannu a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan.

Cov/Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Aiwatarda Najeriya Shirya Yarjejeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi

Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.

Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.

A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.

“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.

Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi