Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah
Published: 20th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) ta yi iƙirarin cewa wasu ’yan bindiga sun sace sama da shanu miliyan huɗu na mambobinta musamman a yankin Arewa maso Yamma.
Shugaban Ƙungiyar MACBAN na ƙasa, Baba Usman ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da sababbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙungiyar na jiha a Jihar Kebbi.
Ya ce, ɓarayin shanu na yawan kai wa Fulani makiyaya hari, lamarin da ke haddasa asarar rayuka da dukiyoyi.
Usman ya jaddada cewa, ana yawan sauya fahimtar Fulani makiyaya da kuma yin kuskuren sanya su a matsayin masu tayar da fitina, inda ya buƙaci jama’a su riƙa ganin su a matsayin ’yan Najeriya masu son zaman lafiya.
Ya kuma yi kira ga makiyaya da su guji shiga gonaki, su kuma zauna lafiya da manoma domin hana rikice-rikice.
Usman ya kuma yabawa gwamnatin tarayya da na jihohi bisa kafa ma’aikatar kiwo, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen magance matsalolin da makiyaya ke fuskanta.
Ya kuma yabawa gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris bisa ayyukan da suka inganta rayuwar al’ummar Fulani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fulani makiyaya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa.
Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum.
A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu.
Gwamnan ya kara da cewa taimakon da aka bai wa waɗannan ƙungiyoyi zai kara habaka tattalin arzikin al’ummar jihar. Ya yabawa ƙungiyoyin bisa yadda suka tsaya tsayin daka wajen kare muradun membobinsu.
Ya bukaci shugabannin ƙungiyar da su tabbatar da sa ido sosai da kuma ganin cewa an bi dukkan sharuddan shirin. “Hakan zai tabbatar da cewa motocin sun yi aiki daidai da manufa, tare da bai wa shirin damar dorewa da kuma faɗaɗawa don amfanar da wasu a nan gaba’. In ji shi.
Gwamnan ya yaba da rawar da NURTW ke takawa a tattalin arzikin jihar, yana mai bayyana su a matsayin muhimmin ɓangare na samar da kayayyaki, ko a fannin noma, masana’antu ko kasuwanci. Ya ce babu wata harkar rarraba kaya da za ta yi tasiri ba tare da haɗin guiwar NURTW ba.
A cewarsa, gwamnatinsa na saka jari mai yawa a fannin gina hanyoyin mota, inda aka kammala ayyukan hanya guda 26 da aka gada, da kudin da ya kai sama da naira biliyan 100. Haka kuma, an ƙara bayar da kwangiloli don gina tituna 50 masu tsawon fiye da kilomita 850, da kudinsu ya haura naira biliyan 300.
Gwamnan ya bayyana cewa an fara amfani da hanyoyin makamashi masu tsafta, inda aka kusa kammala cibiyar sauya motoci zuwa CNG a jihar. Ya ce wannan cibiya za ta taimaka matuƙa wajen rage farashi da kuma tsaftace muhalli, tare da fa’ida kai tsaye ga ƴan NURTW.
A wani ɓangare na shirin, Gwamna Namadi ya kaddamar da tsarin lamuni na naira miliyan 113 ga ƴan kungiyar mahauta. Shirin zai taimaka wa mutane 53, inda manyan ‘yan kasuwar dabbobi 15 za su samu naira miliyan 5 kowanne, sai sauran 38 da za su samu miliyan 1 kowanne.
Ya ce ana sa ran wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar kiwon dabbobi da samar da nama a jihar, har da kasuwannin nama gaba ɗaya.
Don tabbatar da dorewar wannan ci gaba, gwamnan ya bayyana shirin kafa sabuwar ma’aikatar ci gaban kiwo a jihar.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa a matakin farko na shirin, an raba motoci 36 na kasuwanci da darajarsu ta kai naira miliyan 279.3, tare da inshora, ga membobin NURTW karkashin tsarin lamuni na juyi da hukumar Youth Economic Empowerment da Employment ta jihar ke jagoranta.
Usman Muhammad Zaria