Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
Published: 20th, February 2025 GMT
Kungiya mai gwagwarmaya ta Falasdinawa Hamasa ta bayyana cewa tana iya sakin fursinoni yahudawa wadanda suke hannunta gaba daya a lokaci guda a marhala ta biyu ta musayar fursinoni tsakaninta da tare da sharadin ta cika al-kawulan da ta nauyi alhakin aiwatar da shi a wannan karon. Daga cikin har da maida tsagaita wutan na din din din
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Taher Al-Nounou ya cewa idan an yi haka za’a kammala musayar fursononin gaba daya, sannan HKI ta sake duk fursinonin falasdinawa gaba daya da suke hannunta.
Kafin wannan sanarwan dai ministan yaki na HKI Isarael Katz ya bayyana cewa HKI tana shirin shiga tattaunawa ba gaba ba kai tsaye ba, da Falasdinawa a marhala ta biyu da kungiyar Hamas, Ya kuma kara da cewa gwamnatinsa tana samun goyon bayan gwamnatin Amurka.
A zagaye na farko an musayar dai yahudawa 33 Hamas ta saka sannan Falasdinawa kimani 2000 suka sami yanci. Dakarun Qassam kadai ta saki yahudawa 19 a yayinda sauran kuma sauran kungiyoyin kuma sake sauran. A taunawa ta gaba ce za ta fayyace yadda tattaunawa ta gaba zata kasance.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku
Sojojin Yemen sun sanar da kai wasu zafafan hare-hare guda 3 kan mayakan sojojin yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya
Rundunar Sojin kasar Yemen ta sanar da cewa: Sojojinta sun kai wasu jerin zafafan hare-hare guda uku da jiragen saman yakin soji marasa matauka ciki, inda hare-haren suka janyo barna a muhimman wurare uku na makiya sojojin mamayar Isra’ila.
A cikin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta Yemen ta fitar ta bayyana cewa: Wadannan hare-hare wani bangare ne na matakin da ya dace na mayar da martani ga hare-haren wuce gona da iri da sojojin mamayar Isra’ila ke kai wa kan zirin Gaza.
Sannan sanarwar ta kara da cewa: Farmakin na farko an kai shi ne yankin Jaffa da aka mamaye da jirage marasa matuka ciki guda biyu. Harin na biyu ya biyo an kai shi ne kan yankin Ashkelon. Sannan harin na uku an kai ne kan wani gungun sojojin mamaya a yankin Negev.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci