Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang ya ce hare-hare da kashe-kashen da ake yi a wasu sassan jihar wasu ne ke ɗaukar nauyinsu ba rikicin manoma da makiyaya ba ne.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin bikin baje kolin kayayyaki da fasaha da ƙungiyar Tincity Fashion Week ta shirya a daren Juma’a a Abuja.
Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya NAN ya bayar da rahoton cewa, a ranar 2 ga watan Afrilu, wasu ’yan bindiga sun kai hari a ƙauyukan Manguno, Daffo da Josho na ƙaramar hukumar Bokkos ta jihar.
Maharan sun kashe mutane da dama tare da lalata gidaje da wasu kadarori na miliyoyi.
Mutfwang, wanda ya jaddada cewa hare-haren an tsara shi ne, ya yi alƙawarin cewa gwamnati da hukumomin tsaro sun tanadi matakan daƙile afkuwar lamarin nan gaba.
“Ina so in gode muku da kuke nan domin goyon bayanku da kuma karrama Filato tare da halartarku a wannan taron, ba mu ɗauki wannan haɗin kai da wasa ba.
“Mun yi tunanin dakatar da wannan taron ne saboda yanayin tsaro da jihar ke fama da shi, amma mun yanke shawarar kada lamarin ya lalata mana kyawawan abubuwan da ya kamata mu yi na taron biki.
“Kuma dole ne in ce manufar maƙiya ita ce jefa jihar cikin ruɗu da baƙin ciki, amma za mu kauda manufarsu ba za mu ba damar yin abin da suke so ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Caleb Mutfwang
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Idan aka maimaita ta’asar kai hari kan Iran, za ta mayar da martani ta hanyar da ba za a iya boyewa ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya mayar da martani kan barazanar da jami’an Amurka suka yi a baya-bayan nan, inda ya ce idan aka sake kai hari kan Iran, za ta mayar da martani mai tsauri wanda ba zai yiwu a iya boye ba.
Araghchi ya kara da cewa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin din nan cewa: Iran, kasar da ke da al’adun gargajiyar da ta shafe shekaru dubu bakwai na wayewar kai, ba za ta taba mika kai ga barazana da tsoratarwa ba. Iraniyawa ba su taba mika kai ga kasashen waje ba kuma ba su bukatar komai sai girmamawa.
Ya ci gaba da cewa: “Iran ta san hakikanin abin da aka yi mata da kuma abin da makiya suka fuskanta a lokacin farmakin da ‘yan sahayoniyya da Amurka suka yi a baya-bayan nan, ciki har da yawan munanan hare-haren da ta kai a matsayin daukan fansa wadanda ake ci gaba da boyewa. Don haka idan makiya suka sake kuskuren kai hari kan Iran, babu shakka zasu fuskanci martani mai gauni da ba zai yiwu a iya boyewa ba.