Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang ya ce hare-hare da kashe-kashen da ake yi a wasu sassan jihar wasu ne ke ɗaukar nauyinsu ba rikicin manoma da makiyaya ba ne.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin bikin baje kolin kayayyaki da fasaha da ƙungiyar Tincity Fashion Week ta shirya a daren Juma’a a Abuja.
Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya NAN ya bayar da rahoton cewa, a ranar 2 ga watan Afrilu, wasu ’yan bindiga sun kai hari a ƙauyukan Manguno, Daffo da Josho na ƙaramar hukumar Bokkos ta jihar.
Maharan sun kashe mutane da dama tare da lalata gidaje da wasu kadarori na miliyoyi.
Mutfwang, wanda ya jaddada cewa hare-haren an tsara shi ne, ya yi alƙawarin cewa gwamnati da hukumomin tsaro sun tanadi matakan daƙile afkuwar lamarin nan gaba.
“Ina so in gode muku da kuke nan domin goyon bayanku da kuma karrama Filato tare da halartarku a wannan taron, ba mu ɗauki wannan haɗin kai da wasa ba.
“Mun yi tunanin dakatar da wannan taron ne saboda yanayin tsaro da jihar ke fama da shi, amma mun yanke shawarar kada lamarin ya lalata mana kyawawan abubuwan da ya kamata mu yi na taron biki.
“Kuma dole ne in ce manufar maƙiya ita ce jefa jihar cikin ruɗu da baƙin ciki, amma za mu kauda manufarsu ba za mu ba damar yin abin da suke so ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Caleb Mutfwang
এছাড়াও পড়ুন:
Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
Kamfanin Microsoft ya sanar da ƙwace shafukan yanar gizo na wasu kamfanoni 340 a Najeriya bayan samunsu da laifin sarrafa fasahohin kamfanin ba bisa ƙa’ida ba, musamman satar bayanan mutane.
Sanarwar da Microsoft ya fitar ta ce matakin ya biyo bayan wani umarni da wata kotu a Amurka ta bayar tun a farkon wannan wata, wadda ta bai wa kamfanin damar ɗaukar matakin ladabtarwa ga waɗanda ke amfani da fasaharsa ba tare da izini ba.
An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a GombeSteven Masada, mataimakin shugaban sashen lauyoyi na Microsoft da ke kula da laifukan intanet, ya bayyana cewa waɗannan kamfanoni sun ɗauki bayanan abokan hulɗarsu sama da 5,000, inda suka yi amfani da shafukan kutse domin samun bayanan sirri.
A cewarsa, ɗaya daga cikin shafukan da suka fi haddasa damuwa shi ne wani da ake kira Raccoon0356, wanda ke da mabiya fiye da 850 a manhajar Telegram. Wannan shafi ne ke bai wa wasu damar samun kayan aikin kutse don shigar bayanan sirri na Microsoft da wasu hukumomi.
Microsoft ya bayyyana Joshua Ogundipe, mazaunin Najeriya a matsayin wanda ke jagorantar wannan shafi da ke kan manhajar Telegram, kuma bai bayar da amsa a saƙon da aka aike masa ba, don ya kare kanshi game da ayyukan da kamfanin ya ce yana aikatawa.
Kamfanin na Microsoft ya ce ya gano yadda Joshua ya jima tare da ƙwarewa wajen satar bayanan mutane, inda a tsakanin 12 zuwa 28 ga watan Fabrairun wannan shekara, ya yi kutse a shafukan hukumomi sama da 2,300, mafi yawansu na Amurka.