Leadership News Hausa:
2025-07-31@18:28:18 GMT

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

Published: 5th, April 2025 GMT

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

Har ila yau a kan batun haraji, a karshen bara, kasar Sin ta cire harajin kwastan a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa da su daga kasashen da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka, matakin da a hannu guda ya saukaka hanyoyin shigowar amfanin gona na kasashen Afirka cikin kasuwar kasar Sin don biyan bukatun gidanta, a dayan hannu kuma, ya taimaka ga saukaka fatara da ma bunkasuwar sana’o’i a kasashen Afirka.

Wato ke nan, Sin da kasashen Afirka sun tabbatar da cin moriyar juna da samun nasara tare ta hanyar bude kofa da ma hada gwiwa da juna.

Lallai kashe fitilun wasu ba zai taimaka ga samar da haske ga wasu ba. A zamanin dunkeluwar tattalin arzikin duniya, tuni kasa da kasa sun zamanto masu matukar alaka da juna a tattalin arzikinsu, kuma ko kadan ba zai yiwu ba su katse huldar tattalin arziki da juna.

Ba shakka, bude kofa da hadin gwiwa da juna kalmomi ne mafi dadi, wanda a baya an shaida hakan, kuma zai ci gaba da tabbata a gaba. (Lubabatu Lei)

 

 

 

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa tun daga shekarar nan ta 2025 har zuwa 2026.

IMF ya bayyana sabon hasashen a watan Yulin da muke ciki wanda a ciki ya yi ƙiyasin samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya.

Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

Asusun ya yi hasashen samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya da kashi 3.4 a 2025, ƙari a kan hasashen kashi 3.0 da ya yi a watan Afrilu.

Haka kuma, IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai samun ƙarin bunƙasa da kashi 3.2 a 2026, saɓanin hasashen kashi 2.7 da ya yi a watan na Afrilu.

Sai dai duk da wannan, wani rahoto IMF ya fitar a watan Yunin bana, ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.

IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.

A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Nijeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa