Motar Fasinja ta kama wuta wasu sun tsallake rijiya da baya
Published: 5th, April 2025 GMT
Direba da kwandastan motar bas sun tsere domin tsira da rayukansu, inda suka bar fasinjoji a ciki yayin da wata motar bas ta BRT ta kama wuta a Maryland da ke Jihar Legas da safiyar ranar Asabar.
Majiyar Channels TV da ke wajen da lamarin ya faru, ta ce motar ta taso ne daga yankin Ikorodu tana kan hanyar zuwa CMS a lokacin da lamarin ya faru.
Ya zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoton, masu bayar da agajin gaggawa da suka haɗa da jami’an ’yan sandan Nijeriya, da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas (LASTMA), da jami’an kashe gobara da jami’an tsaro na yankin, sun isa wurin domin shawo kan gobarar.
Ɗaya daga cikin fasinjojin motar ta shaida wa majiyar cewa gobarar ta tashi ne a matsayin hayaƙi daga ɓangaren direban.
A cewarta, tun farko fasinjojin sun yi tunanin hayaƙin ya fito daga wasu motocin bas ɗin; duk da haka, ba da daɗewa ba hayaƙin ya ƙara tsananta, hakan ya sa su cikin yanayin firgita.
“Da muka ga hayaƙin ya yi yawa, nan take muka fito daga motar bas ɗin kafin wutar ta tashi”, ta ƙara da cewa babu wani daga cikin fasinjojin da ya samu wani rauni.
Ta ƙara da cewa direban motar ya gudu bayan tashin gobarar.
“Direban da kwandastan sun gudu, ba su ma jira su ga abin da zai same mu ba.
“Tabbas, sun san abin da ya faru, sun san motar bas ɗin ba ta da kyau kafin su saka fasinja su bi hanya kuma sun jefa rayuwarmu cikin haɗari,” in ji ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gobarar bas
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.