Motar Fasinja ta kama wuta wasu sun tsallake rijiya da baya
Published: 5th, April 2025 GMT
Direba da kwandastan motar bas sun tsere domin tsira da rayukansu, inda suka bar fasinjoji a ciki yayin da wata motar bas ta BRT ta kama wuta a Maryland da ke Jihar Legas da safiyar ranar Asabar.
Majiyar Channels TV da ke wajen da lamarin ya faru, ta ce motar ta taso ne daga yankin Ikorodu tana kan hanyar zuwa CMS a lokacin da lamarin ya faru.
Ya zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoton, masu bayar da agajin gaggawa da suka haɗa da jami’an ’yan sandan Nijeriya, da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas (LASTMA), da jami’an kashe gobara da jami’an tsaro na yankin, sun isa wurin domin shawo kan gobarar.
Ɗaya daga cikin fasinjojin motar ta shaida wa majiyar cewa gobarar ta tashi ne a matsayin hayaƙi daga ɓangaren direban.
A cewarta, tun farko fasinjojin sun yi tunanin hayaƙin ya fito daga wasu motocin bas ɗin; duk da haka, ba da daɗewa ba hayaƙin ya ƙara tsananta, hakan ya sa su cikin yanayin firgita.
“Da muka ga hayaƙin ya yi yawa, nan take muka fito daga motar bas ɗin kafin wutar ta tashi”, ta ƙara da cewa babu wani daga cikin fasinjojin da ya samu wani rauni.
Ta ƙara da cewa direban motar ya gudu bayan tashin gobarar.
“Direban da kwandastan sun gudu, ba su ma jira su ga abin da zai same mu ba.
“Tabbas, sun san abin da ya faru, sun san motar bas ɗin ba ta da kyau kafin su saka fasinja su bi hanya kuma sun jefa rayuwarmu cikin haɗari,” in ji ta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gobarar bas
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya zargi Isra’ila da yin zagon kasa ga diflomasiyya ta hanyar tsallaka jajayen layukan kasar Iran, da kuma ta’azzara rikici da kasashen yammacin duniya, yana mai bayyana cewa, ba za a iya yin shawarwari a halin da ake ciki ba.
Sanarwar dai na nuni da koma baya sosai a yunkurin diflomasiyya na Iran da kasashen Yamma, musamman yadda tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara bayan matakin sojin Isra’ila.
Matakin na Isra’ila da hadin kai tare da Amurka na a matsayin kokari na kawar da duk wata dama ta cimma sakamakon shawarwari.
“Ba za a iya shawarwarin ba yayin da a lokaci guda ake barin gwamnatin kisan kare dangi ta kai hari kan Iran.”
“Ba Isra’ila za ta aikata irin wadannan laifuka ba tare da amincewar Amurka ba.”
Iran dai na kallon hare-haren da Isra’ila ta kai a baya-bayan nan a matsayin wani hari kai tsaye ga ‘yan kasarta.