Aminiya:
2025-07-31@14:02:22 GMT

Motar Fasinja ta kama wuta wasu sun tsallake rijiya da baya

Published: 5th, April 2025 GMT

Direba da kwandastan motar bas sun tsere domin tsira da rayukansu, inda suka bar fasinjoji a ciki yayin da wata motar bas ta BRT ta kama wuta a Maryland da ke Jihar Legas da safiyar ranar Asabar.

Majiyar Channels TV da ke wajen da lamarin ya faru, ta ce motar ta taso ne daga yankin Ikorodu tana kan hanyar zuwa CMS a lokacin da lamarin ya faru.

Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe

Ya zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoton, masu bayar da agajin gaggawa da suka haɗa da jami’an ’yan sandan Nijeriya, da hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Legas (LASTMA), da jami’an kashe gobara da jami’an tsaro na yankin, sun isa wurin domin shawo kan gobarar.

Ɗaya daga cikin fasinjojin motar ta shaida wa majiyar cewa gobarar ta tashi ne a matsayin hayaƙi daga ɓangaren direban.

A cewarta, tun farko fasinjojin sun yi tunanin hayaƙin ya fito daga wasu motocin bas ɗin; duk da haka, ba da daɗewa ba hayaƙin ya ƙara tsananta, hakan ya sa su cikin yanayin firgita.

“Da muka ga hayaƙin ya yi yawa, nan take muka fito daga motar bas ɗin kafin wutar ta tashi”, ta ƙara da cewa babu wani daga cikin fasinjojin da ya samu wani rauni.

Ta ƙara da cewa direban motar ya gudu bayan tashin gobarar.

“Direban da kwandastan sun gudu, ba su ma jira su ga abin da zai same mu ba.

“Tabbas, sun san abin da ya faru, sun san motar bas ɗin ba ta da kyau kafin su saka fasinja su bi hanya kuma sun jefa rayuwarmu cikin haɗari,” in ji ta.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gobarar bas

এছাড়াও পড়ুন:

Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya shimfiɗa wa Isra’ila wasu jerin sharuɗan da ya ce idan ba ta cika ba, Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasdinu.

A ranar Talata ne Mista Starmer ya ce idan har Isra’ila ba ta cika waɗannan sharuɗa ba zuwa watan Satumba Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu.

Sharuɗɗan da firaministan ya gindaya sun haɗa da:

Amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta Bai wa Majalisar Dinkin Duniya damar sake shigar da agaji Gaza Amincewa da yuarjejeniyar zaman lafiya na dogon lokaci wanda zai ”samar da ƙasashe biyu” Tabbatar da cewa ba za a ci gaba da ƙwace Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye ba

Haka kuma Keir Starmer ya kuma sake jaddada buƙatun da Birtaniya ke da su kan Hamas da suka haɗa da:

Amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta Sakin duka sauran Isra’ilawan da take riƙe da su Amincewa ba za ta saka hannu a tafiyar da gwamnatin Gaza ba Miƙa duka makamanta

BBC/Hausa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati