Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa
Published: 10th, February 2025 GMT
Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya miƙa wa Majalisar Dokokin jihar sunayen zaɓaɓɓun kwamishinoni 16 domin tabbatarwa.
Shugaban Majalisar, Danladi Jatau ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya gudana ranar Litinin a birnin Lafiya.
Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a NasarawaAminiya ta ruwaito cewa, daga cikin sabbin kwamishinonin da gwamnan ya zaɓa har da tsohon Shugaban Masu Rinjayen a majalisar dokokin jihar, Umar Tanko-Tunga da wani tsohon mamba a majalisar, Mohammed Agah-Muluku.
Kakakin Majalisar ya buƙaci kowane ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun kwamishinonin da su gabatar da kwafi 30 na duk bayanansu daga yanzu zuwa ranar Alhamis tare neman su hallara a gaban majalsiar a ranar Litinin ta makon gobe domin tantance su.
Jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin sun haɗa da Yakubu Kwanta daga Ƙaramar Hukumar Akwanga sai Tanko Tunga daga Ƙaramar Hukumar Awe da Munirat Abdullahi da Gabriel Agbashi duk daga Ƙaramar Hukumar Doma.
Akwai kuma Barista Isaac Danladi-Amadu daga Ƙaramar Hukumar Karu da Princess Margret Itaki-Elayo daga Ƙaramar Hukumar Keana da Dokta Ibrahim Tanko daga Ƙaramar Hukumar Keffi LGA da kuma Dokta John DW Mamman daga Ƙaramar Hukumar Kokona.
Sauran sun haɗa da Aminu Mu’azu Maifata da CP Usman Baba mai ritaya daga Ƙaramar Hukumar Lafia. Sai Mohammed Sani-Ottos daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa da Mohammed Agah-Muluku daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa Eggon da Barista David Moyi daga Ƙaramar Hukumar Obi.
Sai kuma Dokta Gaza Gwamna daga Ƙaramar Hukumar Toto da Barista Judbo Hauwa Samuel da Muazu Gosho duk daga Ƙaramar Hukumar Wamba LGA.
Aminiya ta lura cewa cikin jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin 16 akwai tsoffin ’yan majalisar dokokin jihar guda biyu da tsoffin kwamishinoni 6 da kuma mata uku.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Nasarawa Kwamshinoni
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Gwamna Namadi Ya Nada Sarkin Kazaure Amirul Hajj
Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, ya amince da nadin Mai Martaba Sarkin Kazaure, Alhaji Dr Najib Hussaini Adamu, a matsayin Amirul Hajj na Jihar Jigawa, kuma shugaban tawagar Gwamnatin jihar domin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya sanya wa hannu kuma aka raba wa manema labarai.
Gwamnan ya kuma amince da nadin mambobin tawagar Amirul Hajjin.
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa, mambobin sun hada da Dr. Yusuf Abdurrahman, Babban Limamin Masarautar Hadejia da Alhaji Lawan Ya’u Roni, Talban Kazaure.
Sauran su ne Dr. Mahmoud Yunusa, Sa’in Dutse da kuma Alhaji Adamu Dauda Zakar, Durbin Hadejia.
Sanarwar ta bayyana cewa an yi wadannan nade-nade ne bisa la’akari da irin kwazon da suka nuna a ayyukansu, sadaukarwa, kishin kasa, amana da kuma tsoron Allah.
A cikin sakon taya murna ga wadanda aka nada, Sakataren Gwamnati ya bukace su da su ci gaba da nuna wadannan dabi’u yayin da za su gudanar da wannan muhimmin aiki da aka dora musu, don kara tabbatar da amanar da gwamnatin da al’ummar Jihar Jigawa suka dora a kansu.
Sanarwar ta kara da cewa, ana sa ran tawagar Amirul Hajjin za ta yi aiki kafada da kafada da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa da kuma sauran hukumomin da suka dace a matakin Jiha, Tarayya da na kasa da kasa domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da inganci.
Sanarwar ta bayyana cewa nade-naden sun fara aiki nan take.
Usman Muhammad Zaria