Aminiya:
2025-06-15@13:45:27 GMT

Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa

Published: 10th, February 2025 GMT

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya miƙa wa Majalisar Dokokin jihar sunayen zaɓaɓɓun kwamishinoni 16 domin tabbatarwa.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya gudana ranar Litinin a birnin Lafiya.

Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a Nasarawa

Aminiya ta ruwaito cewa, daga cikin sabbin kwamishinonin da gwamnan ya zaɓa har da tsohon Shugaban Masu Rinjayen a majalisar dokokin jihar, Umar Tanko-Tunga da wani tsohon mamba a majalisar, Mohammed Agah-Muluku.

Kakakin Majalisar ya buƙaci kowane ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun kwamishinonin da su gabatar da kwafi 30 na duk bayanansu daga yanzu zuwa ranar Alhamis tare neman su hallara a gaban majalsiar a ranar Litinin ta makon gobe domin tantance su.

Jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin sun haɗa da Yakubu Kwanta daga Ƙaramar Hukumar Akwanga sai Tanko Tunga daga Ƙaramar Hukumar Awe da Munirat Abdullahi da Gabriel Agbashi duk daga Ƙaramar Hukumar Doma.

Akwai kuma Barista Isaac Danladi-Amadu daga Ƙaramar Hukumar Karu da Princess Margret Itaki-Elayo daga Ƙaramar Hukumar Keana da Dokta Ibrahim Tanko daga Ƙaramar Hukumar Keffi LGA da kuma Dokta John DW Mamman daga Ƙaramar Hukumar Kokona.

Sauran sun haɗa da Aminu Mu’azu Maifata da CP Usman Baba mai ritaya daga Ƙaramar Hukumar Lafia. Sai Mohammed Sani-Ottos daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa da Mohammed Agah-Muluku daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa Eggon da Barista David Moyi daga Ƙaramar Hukumar Obi.

Sai kuma Dokta Gaza Gwamna daga Ƙaramar Hukumar Toto da Barista Judbo Hauwa Samuel da Muazu Gosho duk daga Ƙaramar Hukumar Wamba LGA.

Aminiya ta lura cewa cikin jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin 16 akwai tsoffin ’yan majalisar dokokin jihar guda biyu da tsoffin kwamishinoni 6 da kuma mata uku.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Nasarawa Kwamshinoni

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe

Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.

Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

An kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.

A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.

Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.

Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.

Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.

A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.

“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.

Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.

“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa