Aminiya:
2025-07-31@06:10:26 GMT

Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa

Published: 10th, February 2025 GMT

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya miƙa wa Majalisar Dokokin jihar sunayen zaɓaɓɓun kwamishinoni 16 domin tabbatarwa.

Shugaban Majalisar, Danladi Jatau ne ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya gudana ranar Litinin a birnin Lafiya.

Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a Nasarawa

Aminiya ta ruwaito cewa, daga cikin sabbin kwamishinonin da gwamnan ya zaɓa har da tsohon Shugaban Masu Rinjayen a majalisar dokokin jihar, Umar Tanko-Tunga da wani tsohon mamba a majalisar, Mohammed Agah-Muluku.

Kakakin Majalisar ya buƙaci kowane ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun kwamishinonin da su gabatar da kwafi 30 na duk bayanansu daga yanzu zuwa ranar Alhamis tare neman su hallara a gaban majalsiar a ranar Litinin ta makon gobe domin tantance su.

Jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin sun haɗa da Yakubu Kwanta daga Ƙaramar Hukumar Akwanga sai Tanko Tunga daga Ƙaramar Hukumar Awe da Munirat Abdullahi da Gabriel Agbashi duk daga Ƙaramar Hukumar Doma.

Akwai kuma Barista Isaac Danladi-Amadu daga Ƙaramar Hukumar Karu da Princess Margret Itaki-Elayo daga Ƙaramar Hukumar Keana da Dokta Ibrahim Tanko daga Ƙaramar Hukumar Keffi LGA da kuma Dokta John DW Mamman daga Ƙaramar Hukumar Kokona.

Sauran sun haɗa da Aminu Mu’azu Maifata da CP Usman Baba mai ritaya daga Ƙaramar Hukumar Lafia. Sai Mohammed Sani-Ottos daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa da Mohammed Agah-Muluku daga Ƙaramar Hukumar Nasarawa Eggon da Barista David Moyi daga Ƙaramar Hukumar Obi.

Sai kuma Dokta Gaza Gwamna daga Ƙaramar Hukumar Toto da Barista Judbo Hauwa Samuel da Muazu Gosho duk daga Ƙaramar Hukumar Wamba LGA.

Aminiya ta lura cewa cikin jerin zaɓaɓɓun kwamishinonin 16 akwai tsoffin ’yan majalisar dokokin jihar guda biyu da tsoffin kwamishinoni 6 da kuma mata uku.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Nasarawa Kwamshinoni

এছাড়াও পড়ুন:

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Gwamnan Jihar Filato, Barr. Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa babu wata ƙaramar hukuma a cikin jihar da ƴan ta’adda ko ƴan bindiga ke da iko da ita. Ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ƴan jarida da aka gudanar a sabon gidan gwamnati da ke Little Rayfield, Jos, a ranar Talata.

Gwamna Mutfwang ya ce gwamnatinsa ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar tsaro, musamman ta hanyar farfaɗo da rundunar tsaron cikin gida ta jihar wato Operation Rainbow, domin tallafa wa sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen ganin an dawo da zaman lafiya a sassan jihar da rikice-rikicen ƙabilanci ko na addini suka taɓa. Ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya domin tabbatar da fahimtar juna da daidaiton al’umma.

Gwamnan ya sake jaddada buƙatar kafa ƴansandan jiha, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a faɗin Nijeriya. Ya ce kafa ƴansandan jiha zai bai wa gwamnatocin jihohi damar yin tsari da ɗaukar matakan da suka dace da yanayin tsaron yankunansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamatin Tantance Ayyukan Kananan Hukumomi Na Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ya Isa Sule Tankarkar
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa