Daga Abdullahi Jalaluddeen 

Gwamnatin Jihar Kano ta sha alwashin daukar mataki kan masu yin haya da  babura a fadin jihar.

Mai bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Sufuri, Alhaji Danladi Idris Karfi, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai a Kano.

Ya ce gwamnatin ta lura da yadda aka cigaba da yin haya da babura a cikin birnin Kano, lamarin da ya bayyana a matsayin barazana ga zaman lafiya a jihar.

Danladi Karfi ya jaddada cewa dokar da ta haramta zirga-zirgar babura a matsayin sufuri na haya har yanzu tana nan daram, kuma za a aiwatar da ita sosai, inda ya gargadi masu karya doka da cewa za su fuskanci hukunci mai tsanani.

Ya kara da cewa Kano na daga cikin jihohi mafi zaman lafiya a kasar nan, kuma gwamnati ba za ta lamunci duk wani abu da zai iya tayar da hankalin jama’a ba.

Ya kuma yi kira ga jama’a su kasance masu lura da kai rahoton duk wani abin da suke shakku ga hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Babura

এছাড়াও পড়ুন:

Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban

Asibitin Kula da masu lalurar kwakwalwa da ke Kaduna na Jagorantar Sauye-Sauren Lafiyar ƙwaƙwalwa a Arewacin Najeriya — Farfesa Aishatu Armiya’u Ta Bayyana Muhimman Nasarori a Shugabanci da Ayyuka da Hadin Gwiwa

Shugabar gudanarwa kuma daraktar lafiya ta Asibitin kula da masu lalurar ƙwaƙwalwa dake Kaduna, Farfesa Aishatu Yusha’u Armiya’u, ta tabbatar da kudirin asibitin na ci gaba da jagorantar gyaran tsarin kula da lafiyar kwakwalwa a Arewa, inda ta ce an samu gagarumin ci gaba wajen fafutukar manufofi, kara yawan ayyuka, da karfafa hadin gwiwa tsakanin sassa daban-daban a cikin shekaru uku da suka gabata.

Farfesa Armiya’u ta bayyana cewa horon da ta samu a shirye-shiryen shugabancin harkokin lafiya na Africa ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta salon shugabancinta da kare muradun lafiyar kwakwalwa, da kuma gina ƙwarewa a fannin.

Ta bayyana shirin a matsayin ginshiƙi wajen karfafa mata kwarewar tsara manufofi da aiwatar da gyare-gyaren tsarin lafiya.

Sauya Fasalin Babban Asibitin na kasa dake Kaduna

A matsayinta na shugabar daya daga cikin manyan asibitocin kula da lafiyar kwakwalwa guda goma na tarayyar Najeriya, Farfesa Armiya’u ta jagoranci sauye-sauren da suka mayar da Asibitin Kaduna cibiyar kula da lafiya ta tunani da jiki, bincike, da horas da kwararru a hanya mai dacewa da al’adu.

A karkashin jagorancinta, asibitin ya kafa dimbin yarjejeniyar hadin gwiwa da kungiyoyin cikin gida da na waje don bunkasa lafiyar kwakwalwa ga al’umma.

Daya daga cikin manyan hadin gwiwar ita ce wadda ake yi da Hukumar Rigakafin Shan Miyagun Kwayoyi da Kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa ta Jihar Kaduna wadda ta taimaka wajen samun ci gaba sosai a bangaren manufofi da ayyuka a jihar.

Manyan Nasarorin Manufofi a Jihar Kaduna

Ta hanyar hadin gwiwa da KADSAMHSA, asibitin ya bada goyon bayan fasaha wajen tsara dokoki da tsarin aiki da ake amfani da su wajen sauya fasalin kula da lafiyar kwakwalwa a fadin jihar. Muhimman nasarorin sun hada da:

Sanya magungunan psychotropic a cikin Jerin Muhimman Magungunan Jihar Kaduna na 2025, wanda zai tabbatar da samunsu a cibiyoyin lafiya na matakin farko da na biyu.

Taimakawa wajen tabbatar da dokar Lafiyar ƙwaƙwalwa ta Jihar Kaduna, da amincewa da wata manufa da ke haɗa lafiyar kwakwalwa da cibiyoyin kiwon lafiya na al’umma.

Shirin horaswa da ya kara yawan aikace-aikacensu a fadin jihar, wanda ya bai wa ma’aikatan lafiya 165 horo a manyan asibitoci 15, ciki har da masu kula da samari masu dauke da cutar HIV.

Ta kuma ce asibitin yanzu yana da tsofaffin dalibai 10 na Africa CDC Mental Health Leadership Programme — waɗanda aka horar a Ibadan, Nairobi, da Cairo — kuma kowannensu yana jagorantar muhimman ayyukan gyara.

Inganta Walwalar Ma’aikata da Ingancin Ayyuka

Farfesa Armiya’u ta jaddada cewa jin dadin ma’aikata na daga cikin manyan abubuwan fifiko, inda aka kirkiro sababbin shirye-shiryen da ke inganta lafiyar jiki, tunani da zamantakewa.

Wadannan sun hada da makon lafiya na kowane kwata, wasanni, tarukan zamantakewa, da ingantaccen tsarin inshorar lafiya.

Asibitin ya kuma hade kula da lafiyar jiki cikin ayyukan lafiyar kwakwalwa, tare da kyautata muhalli domin karfafawa da rage wariya.

Wadannan matakai sun kai ga samun babban gamsuwa daga marasa lafiya, inda sama da kashi 90 cikin dari suka bayyana jin dadi da kulawar da suka samu.

Fadada Ayyuka Ta Hanyar Karin Hadin Gwiwa

Asibitin na kara fadada tasirinsa ta hanyar aiki tare da rundunar sojoji, cibiyoyin ilimi, kungiyoyin farar hula, da sauran abokan hulda.

Wadannan hadin gwiwar na taimakawa wajen ba da dama ga karin al’umma su samu kula da lafiyar kwakwalwa a Arewa, tare da karfafa kula da marasa lafiya a cikin al’umma.

Shirye-Shiryen Gaba: Kirkire-Kirkire da Kula da Al’umma

Dangane da makomar asibitin, Farfesa Armiya’u ta bayyana cewa za a kara karfafa tsarin kula da lafiyar kwakwalwa na al’umma, habaka bincike da kirkire-kirkire, fadada amfani da kayan aikin lafiyar kwakwalwa na dijital, da gina karfin ma’aikatan lafiya domin biyan bukatun al’umma da ke ta ci gaba da sauyawa.

Ta jaddada himmar gina tsarin lafiyar kwakwalwa mai tausayi, wanda ba ya takaituwa ga manyan cibiyoyi kawai, kuma ya dace da al’adu — wanda za a iya yada shi a fadin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi