Aminiya:
2025-06-22@18:14:29 GMT

Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai

Published: 6th, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya aika da sakon taya murnar Babbar Sallah ga al’ummar Musulmi, yana kira gare su da su rungumi darajoji na sadaukarwa, biyayya da hakuri irin wanda Annabi Ibrahim (AS) ya nuna.

A wata sanarwa da Daraktan Yada labarai na gidan gwamnati, Ismaila Uba Misilli ya fitar, Gwamnan ya yi kira da a yi addu’o’in zaman lafiya da haɗin kan Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.

Ya jaddada muhimmancin nuna soyayya, tausayi da zama mai ƙyau da maƙwabta a rayuwar yau da kullum.

“Yayin da muke murnar Babbar Sallah, mu yi tunani kan abin da take nufi biyayya, sadaukarwa da ƙwarin gwiwa,” in ji Gwamna Yahaya, yana mai ƙarfafawa al’umma da su ci gaba da tallafa wa shugabanci a matakai daban-daban.

Gwamnan ya yaba wa shugabannin gargajiya da na addini bisa goyon bayansu tare da tabbatar da kudirinsa na kammala ayyukan ci gaba da aiwatar da sabbin manufofi masu alfanu.

Haka kuma, ya taya Alhazai Musulmi murnar kammala aikin Hajji, yana yi musu addu’ar dawowa lafiya da samun albarkar wannan ibada.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babbar Sallah Gwamna Inuwa Yahaya

এছাড়াও পড়ুন:

Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce ba gazawa ba ce ta sa ta yanke shawarar tattaunawa da ’yan bindigar da suka yanke hukuncin ajiye makamansu ba.

Ta ce wannan hanya ce mafi kyau da za ta kawo zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku

Wani mai amfani da kafar sada zumunta, Basharu Altine Guyawa, ya soki wannan mataki na gwamnatin.

Amma Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara kan Tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya ce manufar gwamnati ita ce ta kawo zaman lafiya, ba don ta kasa ba.

Ya ce, “Mun san kowa na da ‘yancin faɗin albarkacin bakinsa. Amma dole ne mu fayyace dalilin da ya sa Gwamna Ahmed Aliyu ke amfani da hanyoyi daban-daban wajen magance matsalar rashin tsaro, ciki har da tattaunawa da ‘yan bindigar da suka tuba.”

Ya ƙara da cewa abin mamaki ne yadda Guyawa ke sukar wannan yunƙuri.

Ya ce shi ma ya taɓa buƙatar shirin shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga domin yin sulhu.

Kanal Usman ya bayyana cewa gwamnati tana amfani da dukkanin matakai biyu; na ƙarfi da na sulhu.

A cewarsa, mutane da yawa a Rabah, Goronyo, Isa, Sabon Birni da wasu yankuna na ta yin hijira.

Manoma sun bar gonakinsu, amfanin gona ya ragu, kuma kasuwanci ya tsaya cak.

Wannan ya jawo ƙarancin abinci da tsadar rayuwa a faɗin jihar.

“Burinmu shi ne mu dawo da zaman lafiya, mu dawo da mutane gidajensu, sannan a sake farfaɗo da harkokin noma da kasuwanci,” in ji shi.

Ya ce har yanzu gwamnati na aike jami’an tsaro inda ya dace.

Amma waɗanda suka tuba da gaske za a karɓe su bisa kulawa da tsari na gyaran hali.

“Wannan ba gajiyawa ba ce ko jin tsoro, wannan dabara ce ta sulhu domin ɗorewar zaman lafiya.”

Amma ya roƙi masu sukar gwamnati da su yi magana cikin hankali.

“Jihar Sakkwato na buƙatar haɗin kai da mafita, ba rabuwar kai da zargi ba. Gwamna Ahmed Aliyu na aiki tuƙuru don kawo zaman lafiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Za mu sake gina kasuwar waya ta Farm Center — Abba
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • Kotu ta aike da dan TikTok din da ke wanka a kan titi a Kano gidan yari
  • Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare