Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
Published: 6th, June 2025 GMT
Gwamna Umo Eno na Jihar Akwa Ibom, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.
Ya bayyana hakan ne a hukumance a ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar da ke Uyo, babban birnin jihar.
Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sandaWannan mataki ya biyo bayan wasu kwanaki da ya shafe yana nuna sha’awarsa na sauya sheƙa.
A wani taron jama’a da aka gudanar a Ikot Abasi, ya ce: “Lokaci ya yi da za mu motsa” domin a haɗa kai da Gwamnatin Tarayya da jam’iyyar APC ke jagoranta.
Gwamnan ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan shafe watanni uku yana tattaunawa da manyan mutane da masu ruwa da tsaki a jihar.
Ya nuna godiyarsa ga PDP saboda goyon bayan da suka ba shi, amma yanzu lokaci ya yi da zai ci gaba da tafiya gaba.
Ya bayyana cewa yana matuƙar ƙaunar Shugaba Bola Tinubu, kuma yana ganin Jihar Akwa Ibom za ta fi amfana idan tana aiki kafaɗa da kafaɗa da Gwamnatin Tarayya.
Gwamna Eno, ya sha alwashin cewa zai ci gaba da yi wa mutanen jihar aiki tuƙuru, ko daga wacce jam’iyya yake.
“Na kammala ganawa da jama’a a matsayin wanda kuka zaɓa, kuma na yanke shawarar komawa jam’iyyar APC,” in ji shi.
Gwamnonin jam’iyyar APC ne suka tarbe shi, ciki har da Gwamnan Jihar Imo kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Hope Uzodimma; Bassey Otu na Jihar Kuros Riba; Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas; da Dapo Abiodun na Jihar Ogun.
Sauran da suka halarta sun haɗa da Gwamna Sheriff Oborevwori na Delta, Monday Okpebholo na Edo, da Francis Nwifuru na Jihar Ebonyi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamna Sauya Sheƙa Siyasa jam iyyar APC
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki
Kungiyoyin ma’aikata na Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna da ke Gidan Waya, Kafanchan sun bayyana aniyarsu na fara yajin aikin gargadi na kwanaki uku.
Sun ce za su shiga yajin aikin ne daga ranar Alhamis, 19 ga watan Yuni, 2025.
Wannan matakin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki 14 da suka yi bai wa gwamnatin jihar, wanda zai kare ranar Laraba, 18 ga watan Yuni.
Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu Ambaliyar Mokwa: Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin NejaAminiya ta rawaito cewa kungiyoyin da suka hada da na Kungiyar Malaman Kwalejojin Ilimi (COEASU), SSUCOEN da Kungiyar Manyan Ma’aikatan Kwalejojin Ilimi ta Najeriya (SSUCOEN) da Kungiyar Ma’aikatan da ba na Koyarwa ba (NASU), na bukatar daukar matakin gaggawa kan batutuwan walwalar ma’aikata da suka ce gwamnati ta yi sakaci da su duk da alkawuran da ta riga ta daukar musu.
Sanarwar ta fito ne daga wani taron manema labarai da Shugaban Hadaddiyar Majalisar Ma’aikatan, Kwamared Alkali Marajos ya jagoranta.
Daga cikin manyan bukatun da kungiyoyin ke nema akwai aiwatar da tsarin albashi na CONPCASS da CONTISS da kuma gyara dokar ritaya ta shekaru 65 don ta shafi hatta ma’aikatan da ba masu koyarwa ba.
Kungiyoyin sun gargadi cewa rashin cika wadannan bukatu zai tilasta musu fara yajin aikin gargadi daga 19 zuwa 23 ga Yuni, 2025.
Sai dai sun sake jaddada aniyarsu ta ci gaba da tattaunawa tare da bukatar gwamnatin jihar da ta dauki matakin gaggawa domin kaucewa tsaiko ga harkokin karatu a makarantar.