Gwamnan Akwa Ibom ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
Published: 6th, June 2025 GMT
Gwamna Umo Eno na Jihar Akwa Ibom, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.
Ya bayyana hakan ne a hukumance a ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar da ke Uyo, babban birnin jihar.
Tinubu ba zai canza Kashim a matsayin mataimakinsa ba a 2027 – APC Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sandaWannan mataki ya biyo bayan wasu kwanaki da ya shafe yana nuna sha’awarsa na sauya sheƙa.
A wani taron jama’a da aka gudanar a Ikot Abasi, ya ce: “Lokaci ya yi da za mu motsa” domin a haɗa kai da Gwamnatin Tarayya da jam’iyyar APC ke jagoranta.
Gwamnan ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan shafe watanni uku yana tattaunawa da manyan mutane da masu ruwa da tsaki a jihar.
Ya nuna godiyarsa ga PDP saboda goyon bayan da suka ba shi, amma yanzu lokaci ya yi da zai ci gaba da tafiya gaba.
Ya bayyana cewa yana matuƙar ƙaunar Shugaba Bola Tinubu, kuma yana ganin Jihar Akwa Ibom za ta fi amfana idan tana aiki kafaɗa da kafaɗa da Gwamnatin Tarayya.
Gwamna Eno, ya sha alwashin cewa zai ci gaba da yi wa mutanen jihar aiki tuƙuru, ko daga wacce jam’iyya yake.
“Na kammala ganawa da jama’a a matsayin wanda kuka zaɓa, kuma na yanke shawarar komawa jam’iyyar APC,” in ji shi.
Gwamnonin jam’iyyar APC ne suka tarbe shi, ciki har da Gwamnan Jihar Imo kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Hope Uzodimma; Bassey Otu na Jihar Kuros Riba; Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas; da Dapo Abiodun na Jihar Ogun.
Sauran da suka halarta sun haɗa da Gwamna Sheriff Oborevwori na Delta, Monday Okpebholo na Edo, da Francis Nwifuru na Jihar Ebonyi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamna Sauya Sheƙa Siyasa jam iyyar APC
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Fubara a Legas
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, a gidansa da ke Legas.
Wannan ganawar na cikin ƙoƙarin warware rikicin siyasa da ya addabi jihar.
Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a KanoFubara, ya samu saɓani da ubangidansa na siyasa, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bayan hauwansa mulki.
Saɓani kan ikon mallakar kuɗin jihar da naɗin muƙamai ya janyo rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin jihar da kuma majalisar dokokin jihar.
A watan Maris 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa, da kuma ‘yan majalisar dokokin jihar baki ɗaya.
Ya naɗa tsohon Hafsan Soja, Vice Admiral Ibokette Ibas (mai ritaya), a matsayin kantoma da zai kula da harkokin jihar.
“Tun da rikicin ya ci gaba da faruwa, babu yadda za a yi gwamnati mai bin doka da ƙa’ida ta ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu a wani jawabi da ya yi.
“Komai ya ta tsaya cak a jihar tun da aka fara rikicin.”
“Gwamnan… ya rushe majalisar dokoki tun ranar 13 ga wata. Disamban 2023, kuma har yanzu bai gyara ta ba,” in ji Tinubu.
“Duk ƙoƙarina na yin sulhu babu abin da ya sauya.”
Duk da cewa ba a bayyana cikakken bayani kan ganawar da suka yi ba, an ce hakan na cikin ƙoƙarin samar da zaman lafiya tsakanin ɓangarorin biyu.
Wannan ganawar ta biyo bayan wata ganawa da suka yi a Landan watanni da suka gabata.
Majalisar Tarayya ta goyi bayan matakin Tinubu, kuma ta buƙaci a kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci cikin watanni shida tare da kafa kwamitin sulhu domin warware matsalar.