Tsawaita Rajistar Sabunta Shaidar Mallakar Fili: Gwamnatin Kano Ta Yi Barazanar Kwace Filaye
Published: 8th, April 2025 GMT
Ya ce karin wa’adin na baya-bayan nan ya biyo bayan cikar wa’adin farko na ranar 1 ga Afrilu, 2025, wanda aka sanya tun da farko a ranar 24 ga watan Janairu.
Umar ya kara da cewa, duk da wannan karin wa’adin, amma an ci gaba da samun karancin fitowar masu filaye domin sabunta takardunsu.
Domin tabbatar da bin ka’ida, kwamishinan ya yi gargadin cewa, nan ba da jimawa ba, za a buga sunayen wadanda ba su bi ka’ida ba a jaridun kasar nan da kuma nuna su a allunan sanarwa a muhimman wuraren gwamnati da suka hada da dakin karatu na jihar Kano, Sakatariyar Audu Bako, Gidan Murtala, da kuma babbar kotun jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Madatsar Ruwan Lagdo na yi wa jihohi 3 na Nijeriya barazanar ambaliya
Rahotanni sun bayyana cewa mazauna wasu jihohin Nijeriya uku na cikin shirin ko-ta-kwana, sakamakon ƙaruwar fargabar samun ambaliya saboda yiyuwar sakin ruwan Madatsar Lagdo ta Kamaru.
A cewar wani rahoto da jaridar Punch ta wallafa, jihohin da mazauna ke cikin zaman ɗar-ɗar sun haɗar da Benuwe da Edo da kuma Bayelsa, waɗanda tuni suka fara shiri don kauce wa barazanar ambaliyar.
Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a JosSai dai Ma’aikatar Albarkatun Ruwa ta Nijeriya ta yi watsi da rahotonnin da ke cewa an buɗe madatsar ruwan, a yayin da tuni jihohin suka fara shirya wa barazanar.
Gwamnatin Benuwe ta ce ta fara aikin wayar da kan jama’a sakamakon ƙaruwar saukar ruwan sama da ake samu a ’yan kwanakin nan.
Jami’ar yaɗa labarai na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa na Jihar Benuwe, Tema Ager ta ce a yanzu haka suna jiran umarni daga ma’aikatar albarkatun ruwa ta ƙasar.
Sai dai ta ce Ministan Albarkatun Ruwan, Farfesa Joseph Utsev, ya yi watsi da rahotanni da ke cewa Gwamnatin Kamaru fara sako ruwa daga Madatsar Ruwan na Lagdo.
Aminiya ta ruwaito cewa, kusan duk shekara dai Gwamnatin Tarayya takan shawarci al’ummomi da ke yankuna a sahun gaba-gaba da su dauki matakan da suka dace domin dakile illar da ka iya haifar da ambaliyar ruwa saboda bude Madatsar Ruwa ta Lagdo.
Da ma duk shekara sai hukumomin Jamhuriyar Kamaru sun saki ruwan Madatsar Lagdo saboda tumbatsar da take yi, abin da kan janyo mummunar ambaliyar ruwa da ke shafar wasu jihohin Najeriya.