Shugaban kwamatin duba rabon abincin azumi na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isiyaku Abubakar ya bukaci masu aikin dafa abincin a karamar hukumar Gwaram da su dauki wannan aiki a matsayin turbar samun lada daga Allah Madaukakin Sarki ba wai hanyar neman riba kadai ba.

Alhaji Sani Isayku Abubakar ya yi wannan kiran ne lokacin da ya jagoranci Yan kwamatin domin duba aikin dafawa da kuma rabon abincin azumi a unguwar Sabon Layi da ke karamar hukumar Gwaram.

Ya ce rangadin duba rabon abincin azumi na daga aikin majalisa na duba ayyuka da shirye-shiryen gwamnati domin tabbatar da inganci da kuma shugabanci nagari.

Alhaji Sani Isayku Abubakar tare da Yan kwamatin sun bukaci mai aikin dafa abincin da ya kara yawan shinkafa da ake baiwa kowanne mutum daya, tare da kayan miya domin samun dandano mai gamsarwa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwaram Farfesa Abdulrahman Saleem Lawan ya ce akwai cibiyoyin rabon abincin azumi guda 22 a mazabu 11, yayin da ya Samar da cibiya ta 23 a gidansa domin mara baya ga kokarin gwamnatin jihar na ciyar da jama’a a watan Ramadan.

Kwamatin ya kuma duba rabon abincin azumi a cibiyar da ke Babban Masallacin Juma’a na Gwaram da ke fadar Hakimin Gwaram.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: rabon abincin azumi

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ce Najeriya na iya ajiye biliyoyin naira a duk shekara idan aka rungumi tsarin majalisa ta wucin gadi.

Yayin da yake magana a gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, Ndume ya ce kuɗin da ake kashewa wajen kula da Majalisar Dokoki a tsarin zama kodayaushe ba zai dore ba, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fama da matsalolin kuɗi da tsaro.

An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra

“Kudin gudanar da gwamnati ya yi yawa sosai. Idan ’yan majalisa suka zauna na wucin gadi, gwamnati za ta ajiye biliyoyi,” in ji shi.

Ya ce za a iya sauya akalar kuɗin zuwa bangaren tsaro da sauran muhimman abubuwan ƙasa.

Ndume ya danganta tsadar gudanar da gwamnati da manyan ƙalubale da ke hana ƙasar yin nasara wajen yaki da rashin tsaro.

Ya ce Najeriya ba za ta iya jure ɓarnar kashe kuɗi ba a yayin da ake fuskantar ta’addanci a Arewa maso Gabas, ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, garkuwa da mutane, da kuma ƙaruwar laifuka.

A wani bangare na fafutukar rage kashe kuɗi, sanatan ya soki ci gaba da kasancewar ’yan sanda da ke tare da sanataci da sauran manyan mutane duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an tsaro daga irin wannan aiki.

Aminiya ta rawaito cewa Shugaban Ƙasa ya umarci Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da ya janye jami’an daga aikin kare manyan mutane ya kuma tura su zuwa fagen yaki da ta’addanci da samar da tsaro.

“Amma har yanzu, ’yan siyasa na tare da ’yan sanda,” in ji Ndume, yana kira ga Babban Sufeton da ya tabbatar da cikakken bin umarnin na shugaban ƙasa.

Ya bayyana cewa tura ’yan sanda daga aikin kare manyan mutane zuwa aikin al’umma da na fagen yaki zai ƙara inganta tsaron ƙasa fiye da ɗaure su ga mutum ɗaya.

Ndume ya ce tsarin tsaron ƙasa ya yi ƙunci kuma yana bukatar “haɗa hannaye wajen yin aiki,” yana mai jaddada cewa dubban jami’an suna makale wajen rakiyar ’yan siyasa da masu tasiri waɗanda za su iya rayuwa ba tare da irin wannan rakiyar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS