Shugaban kwamatin duba rabon abincin azumi na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isiyaku Abubakar ya bukaci masu aikin dafa abincin a karamar hukumar Gwaram da su dauki wannan aiki a matsayin turbar samun lada daga Allah Madaukakin Sarki ba wai hanyar neman riba kadai ba.

Alhaji Sani Isayku Abubakar ya yi wannan kiran ne lokacin da ya jagoranci Yan kwamatin domin duba aikin dafawa da kuma rabon abincin azumi a unguwar Sabon Layi da ke karamar hukumar Gwaram.

Ya ce rangadin duba rabon abincin azumi na daga aikin majalisa na duba ayyuka da shirye-shiryen gwamnati domin tabbatar da inganci da kuma shugabanci nagari.

Alhaji Sani Isayku Abubakar tare da Yan kwamatin sun bukaci mai aikin dafa abincin da ya kara yawan shinkafa da ake baiwa kowanne mutum daya, tare da kayan miya domin samun dandano mai gamsarwa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwaram Farfesa Abdulrahman Saleem Lawan ya ce akwai cibiyoyin rabon abincin azumi guda 22 a mazabu 11, yayin da ya Samar da cibiya ta 23 a gidansa domin mara baya ga kokarin gwamnatin jihar na ciyar da jama’a a watan Ramadan.

Kwamatin ya kuma duba rabon abincin azumi a cibiyar da ke Babban Masallacin Juma’a na Gwaram da ke fadar Hakimin Gwaram.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: rabon abincin azumi

এছাড়াও পড়ুন:

CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara

 

Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwo na Gargajiya ta Afirka (CORET) tare da haɗin gwiwar ECOWAS sun hada matasan da aka horar da su da manyan abokan holda don bunkasa kiyo da bunkasa yawan madara a jihohin Kaduna da Jigawa.

 

A yayin zaman karawa juna sani a Kaduna, Koodinetan Aikin na CORET Dr. Umar Ardo Abdul, ya ce an shirya wannan zama ne domin haɗa matasan da aka horar da su da masu ruwa da tsaki a harkan kiyo da bunkasa yawan madara na gwamnati da masu zaman kansu, domin a horas da su hanyoyin samun aikin yi da kuma bunkasa yawan madara.

 

Wannan shiri na daga cikin Aikin ECOWAS na karfafa samar da ayyukan yi ga matasa da kuma bunkasa darajar madara, wanda yake ɗaukar tsawon shekaru uku, kuma an kaddamar da shi ne domin koya wa matasa ƙwarewar aiki tare da samar musu damar samun kuɗin shiga a cikin fannin kiwo.

 

Koodinetan Aikin, Dr. Umar Ardo Abdul, ya bayyana cewa an yi wa matasa 1,350 rajista a Kaduna da Jigawa.

 

A cewarsa, matasa 26 daga jihohin Kaduna da Jigawa yanzu an haɗa su da masana waɗanda za su tallafa musu a ayyukan yin allurar rigakafi da taimakon lafiyar dabbobi da aikin yaɗa ilimi, da kuma samar da kayan kiwo.

 

Ya yi bayani cewa zaman ya haɗa kwararrun likitocin dabbobi, ma’aikatan yaɗa ilimin kiwo, masu yin dasa ramin maniyyi da masu sarrafa abincin dabbobi da sauran masu ruwa da tsaki a kiwo domin gina ƙaƙƙarfan cibiyar ayyuka.

 

Dr. Umar Ardo ya ce manufar ita ce a tabbatar matasan sun yi amfani da ƙwarewar da suka samu wajen ba da muhimman ayyukan kiwo, samun kuɗin shiga, da kuma tallafawa makiyaya da manoma a yankunansu.

 

Yace ma’aikatar aikin gona ta Jihar Kaduna da Cibiyar Binciken Samar da Dabbobi ta Ƙasa (NAPRI) a matsayin muhimman abokan aikin gwamnati, yana mai cewa NAPRI cibiyar bincike ce da a ke dogaro da ita wajen binciken kiwo, samar da rigakafin dabbobi da kuma kayayyakin kiwo.

 

Koodinetan ya ce gwamnati na da muhimmiyar rawa ta tsare-tsare a fannin kiwon lafiya na dabbobi, rigakafi da kuma samar da kaji, yayin da kamfanonin masu zaman kansu ke taka rawa wajen samar da magungunan dabbobi da kayan kiwo, waɗanda suka zama ginshiƙai ga masu cin gajiyar shirin.

 

Dr. Umar Ardo ya jaddada cewa CORET, a matsayinta na ƙungiyar haɗin kan masu kiwo ta nahiyar Afirka, ta kuduri aniyar cike gibin da ke tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin bincike, kamfanoni masu zaman kansu da matasan da aka horar domin inganta harkar kiwo da bunkasa madara.

 

A nasa jawabin, wakilin Hukumar Ilimin Makiyaya ta Ƙasa, Abubakar Lawal Boro, ya ce tsarin PPP (Haɗin Gwiwar Gwamnati da Masu Zaman Kansu) shi ne ginshiƙin cigaban kiwo mai ɗorewa, domin gwamnati na samar da tsarin aiki da jagoranci, yayin da kamfanoni ke samar da muhimman kayayyaki.

Ya yi kira ga iyalan makiyaya su bai wa ilimi muhimmanci ta hanyar mayar da ‘ya’yansu makaranta, yana nuna damuwa kan yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta da tasirin rashin tsaro ga yunkurin wayar da kai.

 

Ɗaya daga cikin mahalarta, Anas Ibrahim, ya bayyana wannan horo a matsayin mai matuƙar amfani kuma ya zo a kan lokaci.

 

Ya ce zaman ya kasance cikin tsari kuma yana ɗaya daga cikin mafi inganci da suka halarta, inda ya faɗaɗa musu fahimtar lafiyar dabbobi, kula da abincin kiwo, da hulɗa da masu samar da ayyukan kiwo.

 

Wani mahalarta kuma, Rabiu Adamu daga Ladugga, ya yaba wa CORET da abokan aikinta bisa samar da dandalin da ya bai wa masu kiwo damar samun damar magungunan dabbobi masu inganci, abincin kiwo, da iri na kiwo da za su inganta kiwon madara.

COV: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026
  • Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa
  • Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Zargi: Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • Za a aurar da marayu 200 a Zamfara