Shugaban kwamatin duba rabon abincin azumi na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isiyaku Abubakar ya bukaci masu aikin dafa abincin a karamar hukumar Gwaram da su dauki wannan aiki a matsayin turbar samun lada daga Allah Madaukakin Sarki ba wai hanyar neman riba kadai ba.

Alhaji Sani Isayku Abubakar ya yi wannan kiran ne lokacin da ya jagoranci Yan kwamatin domin duba aikin dafawa da kuma rabon abincin azumi a unguwar Sabon Layi da ke karamar hukumar Gwaram.

Ya ce rangadin duba rabon abincin azumi na daga aikin majalisa na duba ayyuka da shirye-shiryen gwamnati domin tabbatar da inganci da kuma shugabanci nagari.

Alhaji Sani Isayku Abubakar tare da Yan kwamatin sun bukaci mai aikin dafa abincin da ya kara yawan shinkafa da ake baiwa kowanne mutum daya, tare da kayan miya domin samun dandano mai gamsarwa.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwaram Farfesa Abdulrahman Saleem Lawan ya ce akwai cibiyoyin rabon abincin azumi guda 22 a mazabu 11, yayin da ya Samar da cibiya ta 23 a gidansa domin mara baya ga kokarin gwamnatin jihar na ciyar da jama’a a watan Ramadan.

Kwamatin ya kuma duba rabon abincin azumi a cibiyar da ke Babban Masallacin Juma’a na Gwaram da ke fadar Hakimin Gwaram.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: rabon abincin azumi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare

Majalisar Dokokin Jihar Akwa Ibom ta ƙi amincewa da wani kudiri da ya nemi haramta ci da sayar da naman kare a jihar.

Kudirin, wanda ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Etinan, Uduak Ekpoufot ya gabatar ranar Talata, bai samu ko da dan majalisa daya da ya mara masa baya ba.

Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi

Jaridar nan ta gano cewa Uduak ya roki majalisar da ta yi la’akari da matsalolin kiwon lafiya da ke tattare da cin nama kare, yana gargadin cewa yadda ake yanka dabbobin ba tare da tsafta ba na iya jefa masu cin nama cikin haɗarin kamuwa da cututtuka irin su rabies, salmonella, trichinella da sauran kwayoyin cuta.

Ya kuma bayyana hanyoyin da ake amfani da su wajen kashe karnuka a kasuwancin a matsayin na rashin tausayi.

Duk da hujjojin da ya gabatar, babu wani ɗan majalisa da ya goyi bayan kudirin, lamarin da ya tilasta wa kakakin majalisar ya yi hukunci da cewa an ƙi amincewa da shi.

Akwai dai sassa da dama na Najeriya, musamman a kudancin kasar nan da ma wasu sass ana Arewacin kasar da ke cin nama kare.

A farkon wannan shekara, wani masani kan namun daji, Edem Eniang, ya ce mata ’yan Najeriya suna cin nama kare fiye da maza, bisa wasu al’adu da ke ɗaukar cewa naman yana inganta laushin fata.

Ya ce wannan al’ada ta fara fitowa fili ne a wata lakca da wani masanin dabbobi, Richard King, ya gabatar.

Eniang ya kuma nuna damuwa kan raguwar adadin karnuka saboda yawan cin naman su da ake yi.

Ya ba da misalan wasu lamarin da suka faru a Ibeno da Oron a jihar ta Akwa Ibom, inda aka sace karnuka aka yanka su don abinci, cikin su har da wata karya mai shayarwa da ’ya’yanta ƙanana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa