Kwamatin Majalisar Jigawa Ya Yi Rangadi A Cibiyoyin Ciyar Da Abincin Azumi
Published: 12th, March 2025 GMT
Shugaban kwamatin duba rabon abincin azumi na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isiyaku Abubakar ya bukaci masu aikin dafa abincin a karamar hukumar Gwaram da su dauki wannan aiki a matsayin turbar samun lada daga Allah Madaukakin Sarki ba wai hanyar neman riba kadai ba.
Alhaji Sani Isayku Abubakar ya yi wannan kiran ne lokacin da ya jagoranci Yan kwamatin domin duba aikin dafawa da kuma rabon abincin azumi a unguwar Sabon Layi da ke karamar hukumar Gwaram.
Ya ce rangadin duba rabon abincin azumi na daga aikin majalisa na duba ayyuka da shirye-shiryen gwamnati domin tabbatar da inganci da kuma shugabanci nagari.
Alhaji Sani Isayku Abubakar tare da Yan kwamatin sun bukaci mai aikin dafa abincin da ya kara yawan shinkafa da ake baiwa kowanne mutum daya, tare da kayan miya domin samun dandano mai gamsarwa.
A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwaram Farfesa Abdulrahman Saleem Lawan ya ce akwai cibiyoyin rabon abincin azumi guda 22 a mazabu 11, yayin da ya Samar da cibiya ta 23 a gidansa domin mara baya ga kokarin gwamnatin jihar na ciyar da jama’a a watan Ramadan.
Kwamatin ya kuma duba rabon abincin azumi a cibiyar da ke Babban Masallacin Juma’a na Gwaram da ke fadar Hakimin Gwaram.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: rabon abincin azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
Karfafa hulda da al’umma da shugabannin yankuna don samun shawarwari kan inganta tsaro.
Ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki don samun nasara a yaki da daba.
Kwamishinan ‘Yansanda ya tabbatar wa mazauna Kano cewa hukumar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyinsu, inda ya ce za su ci gaba da more zaman lafiya ba tare da fargaba ba. Haka kuma, hukumar ta bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani abin da suka gani na zargi ta layukan gaggawa: 08032419754, 08123821575, ko 09029292926.
Rahotanni sun nuna karuwar ayyukan daba a Kano, musamman a cikin birnin, wanda ke janyo asarar rayuka da raunuka ga ‘yan daba da fararen hula.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp