Kwamatin Majalisar Jigawa Ya Yi Rangadi A Cibiyoyin Ciyar Da Abincin Azumi
Published: 12th, March 2025 GMT
Shugaban kwamatin duba rabon abincin azumi na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isiyaku Abubakar ya bukaci masu aikin dafa abincin a karamar hukumar Gwaram da su dauki wannan aiki a matsayin turbar samun lada daga Allah Madaukakin Sarki ba wai hanyar neman riba kadai ba.
Alhaji Sani Isayku Abubakar ya yi wannan kiran ne lokacin da ya jagoranci Yan kwamatin domin duba aikin dafawa da kuma rabon abincin azumi a unguwar Sabon Layi da ke karamar hukumar Gwaram.
Ya ce rangadin duba rabon abincin azumi na daga aikin majalisa na duba ayyuka da shirye-shiryen gwamnati domin tabbatar da inganci da kuma shugabanci nagari.
Alhaji Sani Isayku Abubakar tare da Yan kwamatin sun bukaci mai aikin dafa abincin da ya kara yawan shinkafa da ake baiwa kowanne mutum daya, tare da kayan miya domin samun dandano mai gamsarwa.
A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwaram Farfesa Abdulrahman Saleem Lawan ya ce akwai cibiyoyin rabon abincin azumi guda 22 a mazabu 11, yayin da ya Samar da cibiya ta 23 a gidansa domin mara baya ga kokarin gwamnatin jihar na ciyar da jama’a a watan Ramadan.
Kwamatin ya kuma duba rabon abincin azumi a cibiyar da ke Babban Masallacin Juma’a na Gwaram da ke fadar Hakimin Gwaram.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: rabon abincin azumi
এছাড়াও পড়ুন:
Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi
Majalisar Wakilai za ta ƙada kuri’a a ranakun 10 da 11 ga watan Disamba kan muhimman kudurorin gyaran kundin tsarin mulkin 1999, ciki har da kirkirar sabbin jihohi da kafa ’yan sandan jihohi.
Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Okezie Kalu, ya sanar da jadawalin a zaman majalisar, inda ya ce tattaunawa kan kudirin sauya kundin tsarin mulki za ta gudana yau da gobe kafin kada kuri’ar mako mai zuwa.
An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron NijeriyaKalu, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan nazarin kundin tsarin mulki, ya bukaci ’yan majalisa su halarci zaman.
Ya shaida wa majalisar kwanan nan cewa kwamitin ya kammala aikin da ake bukata a wannan mataki, kuma yana shirin gabatar da takardun da aka daidaita don a yi la’akari da su.
A farko dai an gabatar da jimillar kudirori 87 da ke neman sauya sassa daban-daban na kundin tsarin mulki.
Kudirorin sun shafi gyaran harkokin zabe da shari’a, ’yan sandan jihohi da batutuwan kudi.
Sai dai bayan jin ra’ayin jama’a a matakin jihohi, taron jin ra’ayin jama’a na kasa a Abuja, tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma daidaitawa da kwamitin majalisar dattawa kan kundin tsarin mulki, adadin kudirin da za a kada kuri’a ya ragu zuwa kusan 45.
A ranar Litinin, 24 ga watan Nuwamba, kwamitocin majalisar wakilai da na majalisar dattawa kan gyaran kundin sun gudanar da taron hadin gwiwa da kakakin majalisun jihohi a Abuja yayin da tsarin sauya kundin ya shiga matakin karshe.
Kalu da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, sun shaida wa kakakin majalisun jihohi cewa makomar kudirin sauye-sauyen yanzu ta dogara ne da majalisun jihohi bayan majalisar tarayya ta kammala aikinta. Kalu ya ce taron ya nuna matakin karshe kafin fara kada kuri’a.
Muhimman kudirorin da ake son gyarawaDaga cikin muhimman sauye-sauyen da aka gabatar kirƙirar ’yan sandan jihohi, ware kujeru na musamman ga mata a majalisa, ’yancin tsayawa takara ba tare da jam’iyya ba, karin ayyuka ga sarakunan gargajiya, karfafa ikon majalisar tarayya da ta jihohi wajen kira shugaban ƙasa da gwamnonin jihohi kan harkokin tsaro da sauransu.
Kazalika, wani kudiri na neman sauya kundin domin mayar da gudanar da zaben kananan hukumomi daga hukumar zabe ta jihohi zuwa INEC.
Haka kuma, wani kudiri na neman tabbatar da cewa a kammala dukkan shari’un zabe kafin rantsar da zababbun jami’ai.
Babban kudiri kuma shi ne na neman kafa ’yan sandan jihohi ta hanyar sauya kundin tsarin mulki domin cire su daga jerin dokokin tarayya zuwa jerin dokokin hadin gwiwa.
Masu goyon baya sun ce wannan mataki zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da suka yi yawa kuma suke neman fin ƙarfin ’yan sandan tarayya.
Kallo zai koma majalisun jihohiBayan an kammala kada kuri’a, za a tura kudirin da aka amince da su zuwa majalisun jihohi 36 don samun amincewa.
Aƙalla majalisun jihohi 24 (wato kashi biyu bisa uku) dole ne su amince da shi kafin a tura su ga shugaban ƙasa don ya sanya hannu.
Duk kudirin da bai samu amincewar jihohi ba zai mutu nan take.