Aminiya:
2025-06-23@05:20:09 GMT

Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba

Published: 4th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana mutane zuwa kwasar man fetur daga wata tankar mai da ta yi hatsari a Jalingo, hedikwatar Jihar Taraba.

A safiyar ranar Litinin ne ’yan sanda da jami’an hukumar tsaro ta Sibil Difens (NSCDC), suka ɗauki wannan mataki bayan faɗuwar tankar man a kan babban hanyar Jalingo zuwa Wukari.

Rahotanni sun bayyana cewa faɗuwar tankar man ke da wuya, jami’an tsaron suka isa wurin, inda suka killace wurin domin hana mutane kaiwa inda man yake.

Daga nan ɗauke tankar man da babbar motar ɗauko, aka mayar  wata motar sannan aka tafi da ita.

NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba NDLEA ta cafke madugun fataucin miyagun ƙwayoyi bayan shekaru 17 yana ɓuya

Kakakin Hukumar NSCDC ne jihar, SC Sam Illiya, ya bayyana wa wakilinmu cewa kwamandan hukumar na jihar da kansa ya jagoranci jami’ansa zuwa wurin domin gudanar da aikin.

Kakakinn ’yan sanda na jihar, SP Usman Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Kwasar man fetur Tankar

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki

’Yan Najeriya mazauna ƙasar Isra’ila sun maƙale bayan ɓarkewar yaƙin Iran da Isra’ila. Sun nemi agajin Gwamnatin Tarayya game da kan halin ƙuncin da suka faɗa tun bayan ɓarkewar yaƙi.

Cikin wani rahoto da Jaridar Punch ta wallafa, ’yan Najeriyar sun zargi gwamnati da rashin kai masu ɗauki yadda da ya kamata, inda suka ce tuni sauran ƙasashe suka fara kwashe ’yan ƙasarsu.

Rahoton ya bayyana cewa ’yan Najeriyar sun fi yawa a birnin Ƙudus da Tel Aviv, inda Iran ta tsananta kai hare-hare.

A halin yanzu, mazauna Isra’ilar sun bayyana cewa suna ɓoye ne a wurare da babu tabbas kuma rayuwarsu na cikin haɗari, a koyaushe komai na iya faruwa da su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Singapore: Jama’ar Sin Suna Da Kwarewar Kirkire-Kirkiren Fasahohi
  • Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna
  • An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya