Ku Kyautata Rayuwar Jama’a Ba Kan Kanku Ba — Buhari Ga Gwamnonin APC
Published: 10th, April 2025 GMT
Buhari ya gode wa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu bisa gyaran da aka yi masa a gidansa na Kaduna.
Ya gode wa gwamnonin APC da suka kai masa ziyara domin taya shi murnar Sallah, inda ya ce wasu daga cikinsu ya yi aiki tare da su, yayin da wasu kuwa sabbi ne.
Shugaban gwamnonin kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya ce sun kai ziyarar ne domin nuna godiya da girmamawa da gudunmawar Buhari wajen gina demokradiyya da ƙarfafa jam’iyyar APC.
Uzodinma ya yaba wa Buhari saboda salon shugabancinsa, da yadda ya miƙa mulki cikin natsuwa ga wani shugaban APC, tare da aiwatar da shirye-shirye a fannonin tsaro, noma, ilimi da ababen more rayuwa.
Ya ce a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, APC na samun kwarjini, kuma ya gode wa Buhari saboda goyon bayan da ya nuna masa a bainar jama’a.
Ya kammala da roƙon Buhari da ya ci gaba da bai wa jam’iyyar shawara da jagoranci domin ganin APC ta ci gaba da mulki da kawo wa Nijeriya ci gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta ce akwai kwamitoci guda 30 da aka daurawa nauyin bibiyar yadda ma’aikatu da hukumomin gwamnatin Jihar ke sarrafa kudade domin gudanar da harkokin yau da kullum, gami da ayyukan raya kasa.
Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana hakan lokacin wata ziyarar aiki a karamar hukumar Babura.
Yayi bayanin cewar, an dorawa Kwamatinsa alhakin duba kananan hukumomi domin tabbatar da shugabanci nagari a yankunan karkara.
A cewarsa, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi da suka hada da jadawalin kudaden da karamar hukuma ke samu daga kason arzikin kasa, da littafin hulda da banki,da takardun biyan kudade na voucher da kundin bayanan tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da ritita kudaden gwamnati.
Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar, ziyarar tana bada damar ganawa tsakanin ‘yan kwamatin da masu ruwa da tsaki na kananan hukumomi domin tattaunawa da su, da nufin samar da kyakkyawan yanayin aiki tare tsakanin bangarori daban daban.
Karamin Kwamatin da wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya jagoranta, ya duba aikin noman shinkafa a fadamar Garu da ta Dangoriba da karamar hukumar Babura ta bullo da shi akan Kudi Naira Milyan 49 da dubu 500, inda aka samar da rijiyoyin ban ruwa dari-dari a kowacce fadama.
Alhaji Usman Musari ya kuma yabawa karamar hukumar Babura bisa kyakkyawar aniyarta, ta mara baya ga kokarin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen bunkasa tattalin arzikin matasa ta fuskar hadahadar aikin noma.
A jawabin sa, shugaban karamar hukumar Babura Malam Hamisu Muhammad Garu, ya bayyana ziyarar a matsayin wani sanannen aiki da Majalisa ke yi duk shekara, inda ya yi kira ga ma’aikata da ‘yan majalisar zartaswar karamar hukumar da su bada cikakken hadin kai domin samun nasarar ziyarar.
Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da mataimakan sakatare da Oditoci biyu.
Usman Mohammed Zaria