HausaTv:
2025-04-30@19:53:35 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba

Published: 6th, April 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu nay au zai yi magana kan cewa “Amurka ba zata taba zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da Falasdinawa ba” wanda ni tahir amin zan karanta.

A dai dai lokacinda rikicin gaza ya zama matsalar ta duniya a halin yanzu, da dama daga cikin masana suna ganin gwamnatin Amurka wacce ta kasance mai goyon bayan HKI na asali ba zata kuma zama mai shiga tsakanin don kawo karshen rikicinta da falasdinawa ba.

Dangane da wannan shafin yanar gizo mai suna “Alkhanadik’ ya rubuta wani sharhi dangane da yakin na gaza a jiya Asabar yana cewa, a dai dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka ta kasance bangare babba a cikin haddasa matsaloli ga al-ummar Falasdinu na lokaci mai tsawo , ba zata kuma, zama a lokaci guda mai shiga tsakani don warware wannan matsalar wacce ta zama rikicin kasa da kasa ba.

Saboda ko way a san cewa wanda ya soma yaki ba zai zama mai kuma shiga tsakanin don samar da zaman lafiya ba.

Hakama kamfanin dillancin labaran ISNA na JMI ya nakalto cewa Donal Trump shugaban kasar Amurka yana son ya zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da kuma falasdinawa, a rigimar da aka dauki shekaru fiye da 70 ana yenta, kuma gwamnatocin Amurka da suka shude har zuwa yau suna goyon bayan HKI, idan ba ma gwamnatin Amurka ba, da a halin yanzu babu HKI.

Masana sun kara da cewa gaskiyar al-amarin ita ce, a duk lokacinda Amurka da HKI sun yi maganan sulhuntawa ko kuma magance matsalar falasdinawa to kuwa, sai dai su kara rikita al-amarin Falasdinawa ta wani bangaren ne amma ba zasu taba gyara ba.

Don haka abinda muke gani a halin yanzu, ba bambancin sa da abubuwan da suka faru a baya ba, na tattaunawa a lokacinda ake ruwan wuta a kanku.

HKI tana kisan kiyashi a gaza, tana kuma ci gaba da rusa gidajensu da kuma duk wani gina a gaza, suna kashesu ta hanyar sasu yunwa, duniya tana gani, amma kuma a can washintong wasu suna maganar wai ana kokarin ganin yadda za’a kawo karshen rikicin.

Wannan ba sabon abu bane, an sha yin haka a baya. Na farko a samar da matsaloli sannan a yi amfani da shi, don tursasawa bangaren da ke da rauni don karban sharuddan da suka tsara.

Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 HKI tare da cikekken goyon bayan gwamnatin Amurka ta fara kissan kiyashi a Gaza, inda mafi yawan wadanda ake kashewar mata da yara ne, da kuma sunan kare kanta take wannan kissan. Manufarsu a wannan yakin a fili yake, wanda kuma shi ne share zirin gaza daga Falasdinawa. Don haka labaran da suke fitowa daga washinton a cikin yan kwanakin da suka gabata na cewa tana kokarin ganin an warware matsalar Falasdinawa da HKI, wata dasisa ce ta shirin neman wata kasa ko kuma wurin da zasu kwashi falasdinawa a Gaza, su kaisu can, sannan HKI ta shari zirin na Gaza ta ginawa yahudawan da take kwasowa daga kasashen yamma zuwa yankin gidana zama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.

M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.

Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.

Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”

Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.

Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.

Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba