Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba
Published: 6th, April 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu nay au zai yi magana kan cewa “Amurka ba zata taba zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da Falasdinawa ba” wanda ni tahir amin zan karanta.
A dai dai lokacinda rikicin gaza ya zama matsalar ta duniya a halin yanzu, da dama daga cikin masana suna ganin gwamnatin Amurka wacce ta kasance mai goyon bayan HKI na asali ba zata kuma zama mai shiga tsakanin don kawo karshen rikicinta da falasdinawa ba.
Dangane da wannan shafin yanar gizo mai suna “Alkhanadik’ ya rubuta wani sharhi dangane da yakin na gaza a jiya Asabar yana cewa, a dai dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka ta kasance bangare babba a cikin haddasa matsaloli ga al-ummar Falasdinu na lokaci mai tsawo , ba zata kuma, zama a lokaci guda mai shiga tsakani don warware wannan matsalar wacce ta zama rikicin kasa da kasa ba.
Saboda ko way a san cewa wanda ya soma yaki ba zai zama mai kuma shiga tsakanin don samar da zaman lafiya ba.
Hakama kamfanin dillancin labaran ISNA na JMI ya nakalto cewa Donal Trump shugaban kasar Amurka yana son ya zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da kuma falasdinawa, a rigimar da aka dauki shekaru fiye da 70 ana yenta, kuma gwamnatocin Amurka da suka shude har zuwa yau suna goyon bayan HKI, idan ba ma gwamnatin Amurka ba, da a halin yanzu babu HKI.
Masana sun kara da cewa gaskiyar al-amarin ita ce, a duk lokacinda Amurka da HKI sun yi maganan sulhuntawa ko kuma magance matsalar falasdinawa to kuwa, sai dai su kara rikita al-amarin Falasdinawa ta wani bangaren ne amma ba zasu taba gyara ba.
Don haka abinda muke gani a halin yanzu, ba bambancin sa da abubuwan da suka faru a baya ba, na tattaunawa a lokacinda ake ruwan wuta a kanku.
HKI tana kisan kiyashi a gaza, tana kuma ci gaba da rusa gidajensu da kuma duk wani gina a gaza, suna kashesu ta hanyar sasu yunwa, duniya tana gani, amma kuma a can washintong wasu suna maganar wai ana kokarin ganin yadda za’a kawo karshen rikicin.
Wannan ba sabon abu bane, an sha yin haka a baya. Na farko a samar da matsaloli sannan a yi amfani da shi, don tursasawa bangaren da ke da rauni don karban sharuddan da suka tsara.
Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 HKI tare da cikekken goyon bayan gwamnatin Amurka ta fara kissan kiyashi a Gaza, inda mafi yawan wadanda ake kashewar mata da yara ne, da kuma sunan kare kanta take wannan kissan. Manufarsu a wannan yakin a fili yake, wanda kuma shi ne share zirin gaza daga Falasdinawa. Don haka labaran da suke fitowa daga washinton a cikin yan kwanakin da suka gabata na cewa tana kokarin ganin an warware matsalar Falasdinawa da HKI, wata dasisa ce ta shirin neman wata kasa ko kuma wurin da zasu kwashi falasdinawa a Gaza, su kaisu can, sannan HKI ta shari zirin na Gaza ta ginawa yahudawan da take kwasowa daga kasashen yamma zuwa yankin gidana zama.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
Isra’ila ta kai hare-hare da dama a safiyar Alhamis kan yankunan gabashin Khan Younis, a kudancin Zirin wanda ke nuna yadda isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.
A cewar kafofin watsa labaran Falasdinawa, sama da hare-hare 10 a jere Isra’ila ta kai.
Bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna makamai masu linzami na dira akan wuraren zama a gabashin birnin.
A lokaci guda, tankunan yaki na Isra’ila da motocin sulke sun yi ruwan bama-bamai a yankunan zama a gabashin Gaza.
Sojojin Isra’ila sun kuma lalata gidaje da dama a gabashin birnin Gaza. Kasa da awa daya bayan haka, sojojin gwamnatin sun sake kai hari kan gidajen fararen hula a wannan yanki.
Hakazalika, sojojin Isra’ila na ci gaba da kai hari kan yankunan arewa maso gabashin Khan Younis, da kuma unguwannin Ma’an, Sheikh Nasser, da Joura al-Lout a kudancin birnin.
Wannan mummunan harin sama ya biyo bayan wani mummunan harin bam da ya kashe mutane sama da 109, ciki har da akalla yara 52, a fadin yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita.
Hamas ta zargi gwamnatin Sahyoniya da karya yarjejeniyar tsagaita wuta.
Kungiyar ta yi kira ga bangaroron da suka shiga tsakani a yarjejeniyar tsagaita wutar, wato Masar, Qatar, Turkiyya da Amurka, da su dauki mataki nan take don matsa lamba ga gwamnatin isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci