Gwamnatin Jihar Borno ta nuna matuƙar damuwarta kan yadda wasu matasa ke amfani da kafafen sada zumunta na yanar gizo wajen yin kalamai masu nuna barazana da al’adunmu na rashin ɗa’a da rashin sanin ya kamata.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar yaɗa labarai da tsaron cikin gida ta jihar Borno ƙarƙashin Kwamishinanta Farfesa Usman A.

Tar ta fitar, gwamnatin ta yi Allah-wadai da irin munanan kalamam da suke yi da kan iya haifar da barazana.

An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe ’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyi

Inda ta yi nuni da cewa, waɗannan kalaman sun saɓawa al’adunmu da tsarin rayuwarmu, musamman a shafukan sada zumunta na yanar gizo da ke nuna yadda matasa ke caccakar manyan jami’an gwamnati da munanan kalaman cin zarafi da cin mutuncin tare da ƙalubalantar manufofin gwamnati ba tare da cizawa su hura ba.

A cewar sanarwar wannan halayya da waɗannan matasa ke nunawa abin tur ne kuma ba abin yarda ba ne.

Don haka gwamnatin jihar tana kira ga matasanta da su kiyaye da ɗabi’un da ba su dace da al’adunmu ba.

Sanarwar ta kuma jaddada sunan jihar a matsayin ‘Gidan Zaman Lafiya’, tare da bayyana muhimmancin kiyaye zaman lafiya da juna a tsakanin al’ummominta daban-dabam.

Yayin da take amincewa da ’yancin faɗin albarkacin baki, da gudanar da taro cikin lumana da tsarin mulki ya ba su, gwamnati ta bayyana ƙarara cewa ba za ta amince da keta doka da oda ko kuma keta kundin tsarin mulki ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Ƙofofin gwamnati a buɗe suke a kodayaushe don bayyana koke-koke na jama’a yadda ya kamata da kuma aiki mai ma’ana,” in ji sanarwar.

“Duk mai son bayyana ra’ayinsa, to ya yi hakan amma bisa manufa ta doka, kuma ’yan ƙasa su guji yin kalamai marasa daɗi kana a guji yaɗa labaran ƙarya ko nuna ƙyama domin duk wanda ya karya doka zai fuskanci fushin hukuma.’

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kafafen sada zumunta na yanar gizo

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta

Duk da ƙarin kuɗin wutar lantarki da sabbin dokokin da aka yi don inganta ɓangaren, yawancin ’yan Najeriya na ci gaba da fama da karancin wutar da kuma tsadarta.

Wannan matsalar babu wanda ta bari, daga manyan masana’antu zuwa ƙananan gidaje a sassa daban-daban a Najeriya.

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya sanar cewa gwamnati tana aiki don magance matsalolin, amma duk da haka ’yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan matsalar, wadda ta ƙi ci ta ƙi cinyewa.

A watan Fabrairun 2024, Gwamnatin Tarayya ta sanya hannu kan sabuwar Dokar Wutar Lantarki. Ta bayyana cewa munafar dokar ta haɗa da taimakawa da kuma bai wa jihohi damar samarwa, turawa, da kuma rarraba wutar lantarki na ƙashin kansu ta hanyoyi daban-daban na cikin gida kamar hasken rana da sauransu.

An gano gawar mutum 15 bayan hatsarin kwalekwale a Neja Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP

Kodayake jihohi 11 sun karɓi wannan doka, amma yawancin al’umma da ’yan kasuwa ba su ga wani sauyi  na a-zo-a-gani ba. Hasali ma, kokawa suke yi bisa yawan katsewar wutar lantarki da kuma rashin ƙarfinta.

Ninka kuɗin wutar lantarki sau uku da aka yi wa kwastomomi da ke kan layin Band A, waɗanda aka yi musu alƙawarin samun wutar aƙalla sa’o’i 20 a kullum, shi ma ya bar baya da ƙura.

Gwamnati Tarayya ta bayyana cewa ta janye tallafin wutar lantarki ne domin inganta ɓangaren ta yadda jihohi za su iya samarwa. Haka kuma jama’a za su riƙa samun wuta mai inganci gwargwadon yadda suke biya.

A kan haka ne aka ƙirkiro da tsarin Band A wanda aka ninka kudinsa sau, tare da alƙawarin bayar da wutar aƙalla awa 20 a kullum ga masu amfani da layin.

Amma yawancin mutanen da ke kan Band A sun ce duk da tsadar kuɗin da suke biya, ba su samun wutar yadda aka yi musu alƙawari. Wasunsu ma na zargin cewa ko babu wutar mitocinsu suna ci gaba da lissafa amfani da ita, wanda ke tilasta musu amfani da injinan janareto.

Wata babbar matsala ita ce sama da rabin masu amfani da wutar lantarki a Najeriya ba su da mita, wanda ke nufin kamfanonin rarraba wutar lantarki na canjin si kudin wuta ne bisa ƙiyasi, wanda galibi ke da tsada kuma babu adalci.

Masana’antu suna wahala

Tsawon shekaru, musamman a tun bayan cefanar da ɓangaren wutar lantarki da gwamnatin Najeriya ta yi, har yanzu matsalar ta ƙi ci, ta ki cinyewa.

Masu masana’antu a Kano, misali, suna kashe miliyoyin naira duk wata a kan kuɗin wutar lantarki amma har duk da haka suna dogara ne a kan injinan janareto saboda rashin tabbacin samun wuta.

Wani mai ƙaramar masana’anta a Kano, Yusuf Bello Yakasai, ya ce sama da kashi 60 bisa 100 na ribarsa tana tafiya ne a biyan kuɗin wutar lantarki.

Wani kuma, Habibu Sulaiman, ya ce miliyan biyu yakw biyan kuɗin wuta a duk wata, wanda ke cinye kaso mai tsoka na ribarsa.

Don haka suka yi kira ga gwamnati da ta dawo da tallafin wutar lantarki ga masana’antu.

A Maiduguri, yawancin kasuwanci da sana’o’i, ciki har da masu injinan niƙa da bankuna, suna aiki ne kusan gaba ɗaya da injinan janareto, masu amfani da man dizel, saboda wutar lantarki ta kasa da sa’o’i uku suke samu a kullum. Wasu ma sun sauka daga kan babban layin wutar na ƙasa saboda yawan lalacewar injinansu, sakamakon tsada yawan rashin daidaiton ƙarfin wutae da ke lalata musu kayan aiki.

Masu ƙananan sana’o’i a Kaduna sun bayyana cewa yanzu kuɗin wutar ke cinye sama da kashi 60% na abin da suke samu.

Abraham Benson, wani mai kamfanin buga takardu, ya ce tsadar kuɗin wutar lantarki, tare da tsadar man fetur da sauran kayan aiki, suna sa kasuwanci ya yi wuya.

Ya kuma yi imanin cewa tsarin rarraba Band A zuwa Band D ba adalci ba ne, hasali ma haifar da tsadar kayan aiki yake yi, wanda kuma ke shafar farashin kayan da aka sana’anta.

Kira don ɗaukar mataki

Mazauna jihohin Binuwai da Filato suna da ƙwarin gwiwa cewa samar da wutar lantarki na gida a jihohi zai inganta abubuwa kuma zai rage tsadarta.

A Jihar Legas, wasu kwastomomi da ke kan layin Band A suna ƙorafin tsadar kudin wuta. Kodayake sun ce suna samun wutar akai-akai, amma duk da haka suna neman a sauya su zuwa ƙananan Band, sa’annan a ba kowa mita.

Masana suna kira ga jihohi da su yi amfani da sabuwar dokar kuma su mayar da hankali kan samar da wutar lantarki na ƙashin kansu ta hanyar amfani da albarkatun gida kamar kwal ko hasken rana da sauransu. Sun yi imanin cewa wannan zai sa wutar lantarki ta zama mai araha.

Duk da yawan ƙorafe-ƙorafen,  kakakin Ministan Wutar Lantarki, Bolaji Tunji, ya nace cewa an samu ci-gaba a ɓangaren, yana mai cewa matsalolin da suka yi shekara da shekaru ana fama da su, ba zai yiwu a iya magance su “farat ɗaya ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Matsalar Lantarki: Ga tsada ga rashin wuta