Rashin ɗa’a: Gwamnatin Borno ta gargaɗi masu amfani da shafukan sada zumunta
Published: 6th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Borno ta nuna matuƙar damuwarta kan yadda wasu matasa ke amfani da kafafen sada zumunta na yanar gizo wajen yin kalamai masu nuna barazana da al’adunmu na rashin ɗa’a da rashin sanin ya kamata.
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar yaɗa labarai da tsaron cikin gida ta jihar Borno ƙarƙashin Kwamishinanta Farfesa Usman A.
Inda ta yi nuni da cewa, waɗannan kalaman sun saɓawa al’adunmu da tsarin rayuwarmu, musamman a shafukan sada zumunta na yanar gizo da ke nuna yadda matasa ke caccakar manyan jami’an gwamnati da munanan kalaman cin zarafi da cin mutuncin tare da ƙalubalantar manufofin gwamnati ba tare da cizawa su hura ba.
A cewar sanarwar wannan halayya da waɗannan matasa ke nunawa abin tur ne kuma ba abin yarda ba ne.
Don haka gwamnatin jihar tana kira ga matasanta da su kiyaye da ɗabi’un da ba su dace da al’adunmu ba.
Sanarwar ta kuma jaddada sunan jihar a matsayin ‘Gidan Zaman Lafiya’, tare da bayyana muhimmancin kiyaye zaman lafiya da juna a tsakanin al’ummominta daban-dabam.
Yayin da take amincewa da ’yancin faɗin albarkacin baki, da gudanar da taro cikin lumana da tsarin mulki ya ba su, gwamnati ta bayyana ƙarara cewa ba za ta amince da keta doka da oda ko kuma keta kundin tsarin mulki ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Ƙofofin gwamnati a buɗe suke a kodayaushe don bayyana koke-koke na jama’a yadda ya kamata da kuma aiki mai ma’ana,” in ji sanarwar.
“Duk mai son bayyana ra’ayinsa, to ya yi hakan amma bisa manufa ta doka, kuma ’yan ƙasa su guji yin kalamai marasa daɗi kana a guji yaɗa labaran ƙarya ko nuna ƙyama domin duk wanda ya karya doka zai fuskanci fushin hukuma.’
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kafafen sada zumunta na yanar gizo
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
Sanata Sunday Marshall Katung, wanda ke wakiltar mazabar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, ya sanar da hukuncin da ya yanke na komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yana mai cewa wannan mataki ne da ya dace domin inganta aikin wakilci da kuma tabbatar da ƙarin haɗin kai ga al’ummar mazabarsa.
A cikin wata sanarwa mai taken “Sabon Babin Rayuwa: Saƙon Haɗin Kai da Manufa Ɗaya,” Sanata Katung ya bayyana cewa wannan shawara ta biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da mazauna mazabarsa, jagororin siyasa, iyalansa da abokan aikinsa.
Ya ce, “Wannan sauyin matsayi yana fitowa ne daga niyyar gaskiya ta yin wa mutanenmu hidima cikin inganci, da tabbatar da cewa muryarmu tana da ƙarfi kuma ana jin ta a manyan teburan yanke shawara da ke tsara makomar al’ummarmu.”
Ya ƙara da cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan kiraye-kirayen da aka yi daga sassa daban-daban na mazabarsa, tare da yabawa irin sha’awar da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, suka nuna wajen yin aiki tare da shi domin kawo “ci gaba mai tarihi da ban mamaki” a yankin.
Sanata Katung, yayin canza shekan tare da Hon. Daniel Amos da wasu abokansa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ya nuna gamsuwa da “ayukan ci gaban” jam’iyyar APC a yankin Kaduna ta Kudu, yana mai cewa suna nuna adalci, daidaito, da ci gaba.
Ya ce, “Zamanin warewa da nuna bambanci, musamman a baya-bayan nan, yana gushewa, kuma ana maye gurbinsa da gwamnatin da ke da manufa da haɗin kai.”
“Saboda haka muna matsawa gaba domin tabbatar da cewa waɗannan nasarori sun dore kuma sun yadu zuwa sauran al’ummomi da dama a yankin,” in ji shi.
Sanatan ya kuma roƙi abokai da abokan aiki da ba su goyi bayan wannan mataki nasa ba, da su mutunta ra’ayoyi daban-daban, tare da kaucewa barin siyasa ta kawo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu.
Ya ambaci kalmar Thomas Jefferson da cewa, “Ban taɓa ɗaukar bambanci a ra’ayi na siyasa, addini ko falsafa a matsayin dalilin janye ƙauna daga aboki ba.”
“A tare, mu ci gaba da zama ɗaya a manufa, mu dage da fata, kuma mu mai da hankali wajen samar da makoma mafi kyau ga al’ummar Mazabar Kaduna ta Kudu.”
Sanata Katung ya tabbatar da ƙudurinsa na ci gaba da aiki don haɗin kai da cigaba.
Daniel Karlmax