Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Alhamdulillah mun yi bikin sallah lafiya kalau a garin Rano kamar yadda muka saba duk shekara kowa yana uzurinsa kamar yadda aka saba lafiya. Alhamdulillah an yi ziyarce-ziyarce lafiya gidajen ‘yan’uwa da surukai da abokan arziki da kuma haduwa da tsofaffin dalibai.

Gaskiya sai godiya duba da yadda ake cikin tsadar rayuwa da wani irin hali na kuncin rayuwa a wannan a kasa ta mu sai dai mu a yankinmu na karamar hukumar Rano muna cikin alhinin kisan gillar da aka yi wa ‘yan’uwanmu a yankin kudu a jihar Edo ba zamu tava manta wannan aika-aika da aka yi mana ba Allah ya isar mana, Allah ya sa mudace Allah yasa mun yi ibadu karvabbu Allah ya maimaita mana masu amfani.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Bikin sallah ya kayatar da mu sosai sai dai wasu ba kamar yadda suka saba duk shekara ba, musamman yadda sallar ta zo ba tare da wasu sun kammala shiri ba. Na ziyarci ‘yan’uwa na na kusa da na nesa kamar Babbar Yayata, Kawu na, Aunty na, dan har garin Kano mun ziyarta, sai wuraren shakatawa, gidajen tarihi, da kuma gidan Sarki. Sallar bana za a ce da ita ma sha Allah Alhamdulillahi, an yi ta cikin zaman lafiyya da kwanciyyar hakali, mun yi kallon hawa.

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Alhamdullilah Ma sha Allah, hakika mun gudanar da bikin sallar idi da shagulgulan bikin sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, al’umma sun yi hidimar sallah daidai gwargwado duk da halin da ake ciki na matsin tattalin arzikin da tsadar rayuwa, fatan mu Allah ya karvi ibadar mu bakidaya. To maganar zuwa ziyara hakika mun ziyarci gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki an gaisa an yi zumunci sosai kai har ma mun samu damar zuwa garuruwan ‘yan’uwa dake nesa domin sada zumunci. To batun sallah sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah tunda mun samu damar gudanar da sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali domin koda ba a samu damar yin hidima mai yawa ba tunda aka samu damar gudanarwa cikin lumana dole mu godewa Allah daya ba mu wannan dama, daga karshe nake kara addu’ar Allah ya karvi ibadar mu ya yafe mana kura-kuran mu don darajar fiyayyen halitta manzon Allah (S.A.W).

Sunana Hafsat Yusuf Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto:

Hidimar wannan sallar ta zamo mai kayatarwa a garin mu duk da matsalar tsaron da ake fama da ita a yankin, mun kai ziyara ga ‘yan’uwa kuma mun hadu da wadanda muka dade ba mu hadu da su ba, abun akwai burgewa. Daga karshe ba abun da zan ce sai Alhamdulillah Allah ya maimaita mana.

Sunana Yasar Saleh Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Yadda bikin sallah yake kasancewa a garin mu sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah. Da zarar gari ya waye kowa da kowa zai fita filin idi dan gabatar da sallah da an sakko za ai ta kai ziyara zuwa gidan ‘yan’uwa da abokan arziki; yayye, kanne da ‘yan’uwa da abokan arziki. To sai godiyar Allah amma kam ta zo wa mutane da yanayi na tsadar rayuwa da matsin tattalin arzikin da muke fama da shi amma duk da haka Alhamdullilah tun da mun samu damar gudanar da bikin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Sunana Fatima Ibrahim Jihar Katsina:

Bikin sallah dai a unguwar da nake ya kasance abu ne mai ban sha’awa, mun je gurare da dama kamar gidan zoo, gurin wasa, gidan ‘yan’uwa da abokan arziki da gidan makama. A gaskiya dai wannan sallar za a iya cewa ta zo kwatsan dan wadansu basu tanadi dinkin sallah ba da kuma lalle da sauransu, ni dai na samu nayi da wuri komai kalau a wajena.

Sunana Fatima Nura Kila, A jihar Jigawa:

Alhamdulillah mun yi sallah lafiya inda kowa yake cikin farin ciki a wannnan rana ta sallah duk da yanayin da ake ciki, amma mutane sun yi ado daidai wadaitar kowa, fatanmu Allah ya nuna mana wata sallar. Alhamdulillah mun yi ziyarar ‘yan’uwa da abokan arziki mutanan da aka dade ba a hadu ba mun kai musu ziyara Yayin da kowa yake farin ciki da ziyarar juna. Wannnan sallar sai dai mu ce Alhamdulillah domin an samu zaman lafiya mun yi ta cikin nutsuwa,walwa da kaunar juna, Ubangiji ya karvi ibadunmu ya kai mu wata shekarar mai albarka ya sa muna raye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arziki yan uwa da abokan arziki cikin nutsuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49

Jami’in tafiyar da sha’anin Mulki a yankin Cape ya fada a jiya Laraba  cewa; An sami karuwar wadanda su ka rasa rayukansu ya karu zuwa 49.

Shugaban tafiyar da sha’anin Mulki a yankin na garin Cape, Oscar Mobyan  ya bayyana haka ne a wani taron manema labaru,kamar yadda kamfanin dillancin labarun Reuters ya nakalto.

Wasu yankuna na kasar ta Afirka Ta Kudu sun fuskanci saukar ruwa kamar da bakin kwarya, haka nan kuma saukar kankara, da hakan ya sa aka shiga cikin yanayin sanyi mai tsanani da kuma yankewar wutar lantarki a wasu yankunan.

Ambaliyar ruwan da aka samu a kusa da wata makaranta ya ja motar da take dauke da dalibai 13, da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu. Tuni an tsamo gawawwakin dalibai shida,ana kuma ci gaba da neman sauran.

Sauyin yanayin duniya yaa shafi kasar Afirka Ta Kudu, ta yadda a cikin shekarun bayan nan ake yawan samu ambaliyar ruwa. A watan Aprilu na 2022 an yi mamakon ruwa  guguwa mai karfi wacce ta ci rayukan kusan mutane 400.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49