Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji
Published: 6th, April 2025 GMT
Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji a zirin Gaza, bayan da wasu sabbin hujjojin bidiyo suka nuna yadda sojojin Isra’ila suke harbin motocin daukar marasa lafiya.
Bidiyon da ya ci karo da wani nau’in lamarin da sojojin Isra’ila suka yi cewa “an gano wasu motoci marasa da yawa suna tunkarar sojojin Isra’ila ba tare da fitillu ko alamun motocin ambullance na gaggawa ba”.
Shugaban kungiyar agajin ta Falasdinu Younes al-Khatib, ya bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kashe-kashen, yana mai jaddada cewa ba za a iya amincewa da binciken da sojojin Isra’ila ke jagoranta ba.
“Ba mu amince da duk wani binciken da sojojin suka yi ba, kuma wannan ne ya sa muka fito fili a kan cewa muna bukatar bincike mai zaman kansa kan lamarin,” in ji al-Khatib a wani taron manema labarai a hedkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York, yayin da yake magana kan harin da ya kashe likitoci da ma’aikatan jin kai 15 a Gaza.
Ya yi Allah wadai da karuwar hare-haren da ake kai wa ma’aikatan jin kai da wuraren aikinsu, yana mai jaddada cewa ana kai hari kan tambarin kungiyar agaji ta Red Crescent, wanda ya kamata a kiyaye a karkashin dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
Ya ce, masu garkuwa da mutanen sun afka gidansa ne a daren Lahadi a lokacin da mazauna gidan ke shirin kwanciya barci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp