Sudan: Ana Ci Gaba Da Yin Fada Tsakanin Sojoji Da Rundunar Daukin Gaggawa A Um-Durman
Published: 5th, April 2025 GMT
Sojojin Sudan suna ci gaba da bata-kashi da dakarun rundunar kai daukin gaggawa a yammaci da kudancin birnin Umdurman.
Majiyar gwamnatin Sudan ta fada wa manema labaru cewa; An dauke mazauna yankin da ake fadan a birnin Umdurman da adadinsu ya kai 5,000 zuwa arewacinsa.
A lokaci daya kuma sojojin na Sudan suna ci gaba da abinda su ka kira da “Shara” a yankin “Jabalul-Auliya” dake kudancin birnin Khartum.
A can birnin Al-Fasha, jiragen saman sojojin Sudan suna kai hare-hare akan wuraren dakarun kai daukin gaggawa a cikin birnin, da hakan ya haddasa asarar ta rayuka da kuma kayan yanki.
A cikin kwanakin bayan nan sojojin Sudan suna samun nasara akan dakarun kare daukin gaggawa da ya hada da korarsu daga birnin Khartum da wasu muhimman birane da su ka hada da Jazira.
Tun a cikin watan Aprilu na 2023 ne dai kasar Sudan ta fada cikin yakin basasa, bayan da dakarun rundunar kai daukin gaggawa su ka mamaye wasu cibiyoyin gwamnati.
Ya zuwa yanzu dai adadin wadnada su ka rasa rayukansu sun wuce 20,000, yayin da wasu miliyan 15 su ka zama ‘yan hijira.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: daukin gaggawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.