Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 105
Published: 5th, April 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na Kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin al-kur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da Littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin Rumi, ko kuma cikin wasu littafan.
///.. Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan lamami na biyu daga limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All…(s) kuma da na farko ga Fatimah (s) diyar manzon All..(s).
A cikin shirimmu da ya gabata, mun yi magana kan yadda aka zabi Khalifa na uku Uthman bin Afffan a matsayin khalifa, a dai dais aura kadan lokacinda Khalifa na biyu ya ware-masu na su zabi daya daga cikinsu a sare wuyoyin su.
Abdurrahman dan Auf wanda shi ne shugaban kwamitin ya rasa abinda zai yi, yayi ta neman shawara daga mutane daban daban. Kowa da abinda yake fada masa. Ammar dan Yasir ya ce masa idan yana son hadin kan musulmi to ya zabi Aliyu dan Abitalib(a) . wasu kuma sun ce masa idan yana son hadin kan kuraishawa to ya zabi Uthman dan Affan. Wannan haka ya ci gaba da faruwa, har zuwa lokacinda Sa’ad dan Abi wakkas ya zo kusa ya fada masa cewa ya yi saura a yanke wannan jayayyar ya zabi daya daga cikin wadannan mutane biyu.
A nan ne sai ya zo kusa da Aliyu dan Abitalib (a) yace masa, zan yi maka bai’a tare da sharadin zaka yi hukunci da littafin Allah da sunnar manzon All..da kuma ayyukan Abubakar da Umar. Sai Ali(a) ya bashi amsa da cewa, sai da littafin All..da sunnan Manzon All..da kuma ijtihadi na da ra’ayi na.
Sai abdurrahman yayi kokarin gamsar da shi ya amince da hakan, amma ya ki amincewa. Sai kawai ya koma wajen Uthmanu, ya bijiromasa sharuddan da ya bijirowa Aliyu (a). sai ya ce ka kawota da dukkan sharuddanta na amince. Sai Abdurrahman yayi masa bai’a a matsayin khalif ana hudu.
Aliyu dan Abitalib (a) bai ji dadi ba, sai ya zo ya fadawa Abdurrahman kan cewa yayi wa Uthman bai’a ne don ya mayar masa da ita wata rana, sai yayi addu’a , yana cewa All..kada ya daidaita a tsakaninsu.
Daga nan sai Aliyu (a) ya juya ta fita daga cikin masallaci ko wurin taron. Wannan duk yana faruwa a gaban Imam Hassan (a). Ya ga a wannan karomma yadda aka hana babanshi hakkinsa, wanda All..ya bashi. Daga nan Magana ta kare, Uthman ya zama khalif ana ukku. Amma wani irin shugabancin ne Uthman yayi?
Malaman tarihi da dama sun bayyana cewa uthman ya karbi Khalifanci ne kawai amma ya barwa Marwan dan Hakan dan amminsa kuma surukinsa yana tafiyar da al-amura al-ummar musulmi.
Shugabancinsa na ciki da matsalolin. Banda haka sanadiyyar yadda ya tafiyar da shugabancinsa al-ummar musulmi ta fada cikin matsaloli, kafin a kashe shi da kuma bayan kisansa har zuwa yau shekaru kimani 1400 da suka gabata, musulmi suna dandana, musibar abinda shugabancin Khalifa Uthman ya jawo, kuma har tashin kiyamah.
Matsala ta farko wacce Khalifa Uthman ya fara fuskanta ita ce. Ubaidullah dan Umar dan Khalifa Umar ya dauki makami ya je ya kashe Hurmozan, da Jufainatu da kuma diyar Abu Lulu’a don daukar fansar kissan mahaifinsa Khalifa na biyu. Wadan nan da ya kashe ba sune suka kashe babansa ba, wanda ya kashe babansa shi ne Abu lulu’a shi kuma ya gudu ya bar gari.
Wasu kuma sun ce wasu sahabban manzon All..(s) sun kashe shi, amma babbar matsala ita ce kissan da Ubaidulahi dan Umar yayiwa, Hurmozan, da Jufainah da kuma diyar Abu Lulul’i. don basu da hannu wajen kashe Khalifa Umar.
Har’ila yau wannan kissar ta faru ne kafin a zabi Khalifa na ukku bayan da Abu lulu’I ya soki Khalifa da wuka a masallaci yana bada sallah, kafin a zabi khalif ana uku.
Don haka matsala ta farko wacce ya fuskanta ita ce batun hukuncin Ubaidullah dan Umar, wasu sahabban manzon All..(s) sun dage kan cewa sai an yi kisasi kan Ubaidullah, saboda kissan da gangan ce. Daga cikin wadanda suke da wannan ra’ayin akwai amirulmuminina Aliyu dan abitalib (a).
Don haka Khalifa Uthman ya nemi shawarar sahabban manzon All..(s) da dama, wasu suce ya yi kisasi wasu kuma su ce ya biya diyya, wasu sun ce masa ta yaya zai kashe dan Khalifa Umar a yau bayan an kashe babansu a jiya. Wasu kuma sun ce masa a wajen yin kisasi shi ya dace, don kada wani dan babban gida ya sake irin wannan, ya zama idan mutum ya fita daga gidan babban mutum sai a ki yi masa hadda, amma in dan talaka ne sai a zartar da haddi a kansa, da sauransu.
Amma Amru dan Asi ya bashi shawara kan cewa.:
A lokacinda ubaidulla kashe wadannan mutane, kai ba khalifa bane, don haka kada ka sa kanka cikin matsala, kayi duk abinda zaka yi da shi in banda kisa.
A nan khalifa ya karbi shawarar dan Ass, ya ce zai biya diyyar kissan Hurmuzan, daga cikin kudinsa ba na Baitul mali ba, sannan ya bada umurnin a saki Ubaidullah dan Umar wandakafin haka ana tsare da shi a gidan yari.
Amma wasu sahabban sun ci gaba da yi masa barzana kan cewa duk sanda aka sami dama sai an zartar da haddin kisasa a kansa.
Daga cikinsu akwai Ziyad dan Lubaid, wanda Ubaidullah ya kai kararsa gaban Khalifa, uthman wanda ya kira shi ya kuma ce masa kada ya sake.
Daga karshe dai Khalifa ya ce masa ya bar madina ya koma Kufa da zama, ya bashi gida a can har lokacinda al-amura zasu lafa. Da haka aka wuce maganar Ubaidullah dan Umar.
Malaman addinin musulunci a tsawon tarihi sun yi ta sabani a tsakaninsu dangane da yadda Khalifa na uku ya warware maganar kissan Hurmuzan da Juhainatu da kuma diyar Abu lulu’a a farkon khalifancinsa.
Wasu suna ganin alkawalin da Khalifa Uthman ya dauka daga Abdurrahman dan Auf na cewa za iyi hukunci da littafin All..da sunnar manzon All…(s), ya sabawa masu a hukunci na farko da yayi a farkon Khalifancinsa.
Suna kafa hujja da hadisin manzon All..(s) wanda yake Magana a kan zartar da haddin All..a kan talaka da masu arziki, kuma ya nuna masu a aikace kan wani ko wata da tayi sata kuma wanda ya fito daga babban gida. Don haka ya zartar da hukunci All..a kanta. Sannan yace.. da Fatimah(s) diyar Muhammadu (s) zata yi sata da ya yanke hannunta.
Amma Taha Hussain sanennen marubuci dan kasar Masar ya na ganin a wannan halin, matakin da khalifa Uthman ya dauka shi ne dai dai, don a musulunci manzon All..(s) ya bada umurnin a yi watsi da haddi ko da da Shubha ne, yace ana iya daukar shubaha a nan kasancewar ubaidullahi dan Umar yana cikin fushi a lokacinda ya kashe wadannan rayuka guda uku.
Amma idan mun dawo kan Imam Hassan (a) a zamanin Khalifa Uthman, zamu ga cewa a lokacin shi matashi ne dan shakara kimani 20 a duniya. Wasu malaman tarihi sun bayyana cewa, Imam Hassan (a) ya je yaki karkashin rundunar Ukbatu dan Nafiu, da Abdullahi dan Nafiu, zuwa afrika kuma sun sami nasara yada fadada daular musulunci a lokacin har zuwa mafi yawan arewacin Afrika.
Sannan daga baya Abdullahi dan Abisarkh ya nemi izinin Uthman ya kara fafada daular musulunci a arewacin Afirka, sai ya bashi izini, ya kuma kara masa sojoji. Abdullahi dan Abisarkh ya fadada daulara a wasu yankuna.
Wasu malaman sun bayyana cewa a cikin rundunar Akwai, Amr dan Ass, Abdullahi dan Jaafar, da Alhassan da Alhussain (a). kuma sun sami nasara a yankin.
Hakama sun fito yaki zuwa Tabriztan a cikin kasar farisa a lokacin ina shima suka sami nasara.
Sai dai akwai wasu malamai suna musanta cewa Imam Alhassan da Imam Alhussain sun je yaki fadada daular musuluni a zamanin khalifa Uthman kamar yadda muka ambata.
Hakama marubucin littafin futuhatul Islamiyya, bai kawo labarin cewa Alhassan da Alhussain (a) sun je yake-yaken futuhat a zamanin khalif ana ukku a arewacin afrika ba. Amma ya kawo cewa sun halacci yakin Tabristan na kasar Farisa a lokacin.
Ynazun kuma sai siyasar dukiya a zamanin khalifa na uku, wanda yake da bambanci so sai idan an kwatanta da wadanda suka gaba ceshi. Khalifa na farko ya ci gaba da raba kudi kamar yadda manzon All..(s) yake yi a mafi yawan lokuta. Amma khalifa na biyu shi ne ya samar da matakai-matakai a tsakanin musulmi, kamar yadda muka fada a baya.
Asalin rabon kudi a musulunci, kamar yadda Amirulmuminina (a) ya fadawa Abdullahi dan Zam’ah a lokacinda ya zo masa a lokacin khalifancinsa.yace masa (wannan dukiyar nan aka b aba nawa bane, wannan dukiyar na musulmi ne, wanda takubbansu suka samar da su, idan ka yi tarayya da su a yakin da suka yi, kaima kana da rabo kamar yadda suke da shi a cikinsa, in ba haka ba, abinda suka samar ba zai zama rabon waninsu ba.).
Banda haka ya rubutawa walinsa a Makka Kathum ibn Abbas, y ace masa: ka duba cikin abinda ka tar ana dukiya, ka raba shi cikin wadanda suke da iyali mai yawa, da kuma wadanda suke fama da yunwa. Ka tabbatar da cewa ka bawa wadanda suke fama da talauci …sannan abinda ya rage ka aiko mana don mu rabawa wadanda suke wajemmu..
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan all..ya kaimu wassalamu alaikum warhamatullahi wa barakatuhu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ubaidullah dan Umar Khalifa Uthman ya khalifa Uthman ya wadanda suke wasu kuma su masu sauraro kamar yadda
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
Rayukan al’umma gami da dukiya musamman na ababen hawa na ci gaba da salwanta a Mahadar hanya ta yankin Tipper-garage da ke Dutse-Baupma, da ke kan titin da ya tashi daga garin Dutsen-Alhaji ya nufi garin Bwari, a yankin Birnin Tarayya Abuja.
Titin da ke mastayin tagwaye ya haɗa yankin da garin Jere da ke Jihar Kaduna.
Hanyar na ci gaba da ganin ƙaruwar kwararan motoci a sakamakon ingancinta da kuma karancin matsalar tsaro, idan a ka kamanta ta da babban titi Abuja zuwa Kaduna.
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027 An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifasAdadin motoci da ke bin titin ya kara dagawa a bayabayan nan a dalilin mummunan cunkushewar hanya da ake fuskanta a garin Zuba Abuja da kuma Madalla da ke Jihar Neja, a sakamakon rufe hannu guda na hanyar biyo bayan fara aikinsa da wani sabon kamfani ke yi, bayan karbe aikin daga kamfanin Bega.
Baya ga motoci na matafiya da ke yawan ratsawa ta hanyar, akwai kuma motocin tifa da ke daukar duwatsu daga kamafanonin fasa duwatsu biyu da ke kusa da mahadar hanyan suna kai wa yankuna daban-daban na Abuja dama kewaye.
Aminiya ta ba da labarin cewa hatsarin mota na baya bayan nan da a ka fuskanta a hanyar su ne wanda ya auku a ranar Asabar 5 ga wannan watan na Afrilu, 2025, inda a ka rasa rayukan mutum biyar, bayan wata babbar mota tirela da ta fito ta kusurwan Bwari ta fuskanci matsalar tsinkewar birki a yayin da ta ke gangarowa daga hayin madatsar ruwa na Usuma dam da ke kan titin.
Tirelar ta taka kekunan adaidaita sahu guda biyar da ke daukar fasija a gefen hanayar, baya ga wani adadi na baburan acaba.
Kwana biyu bayan aukuwar hatsarin, an sake fuskantan wani a ranar Litinin da ta biyo baya inda wata babbar mota irin ta daukar bulo da ke dauke da albasa daga wata jiha ta Arewa ta rasa birki a yayin saukowa daga gangarar hanyar.
Ta buge kekunan kafin ta kife a kusa da wani magudanan ruwa da ke jikin hanyar.
An bada labarin rasa mutum biyu a yayin hatsarin, baya ga wasu da su ka tsira da raunuka.
Asarar rayuka da ta dukiya da muka yi — Masu tukin adaidaita sahu
Malam Fahad Musa na cikin shugabannin kungiyar ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin Keken Adaidaita sahu da ke aiki a wurin.
Ya ce hatsarin farko ya faru ne da misalign karfe 7 na dare inda ya ce sun rasa mambobinsu uku, sai kuma dan acaba guda, a yayin da mutum na biyar din kuwa ya rasa ransa ne a dalilin harbinsa da bindiga da ake zargin wasu da suka taho cikin ayarin motoci suka yi, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka shaidawa Aminiya.
Shugaban na ’yan yuniyon ya shaida wa wakilinmu a yayin ziyara a wajen cewa an kuma rasa kekune biyar a yayin hatsarin bayan motar ta bi ta kansu.
Ya ce faduwar motar ta farko ta yi sanadiyyar rufe hannu guda sannan ba a kai ga cire ta ba sai bayan hatsari na biyu a ranar Litinin.
Ya ce, a lokacin da ake kokarin zakulu mutane da suka mutu da kuma wadanda suka yi raunukan daga karkashin ababan hawan a ranar Asabar, an rufe daukacin tagwayen titin biyu da lamarin ya kai ga jawo takaddama bayan ayarin jami’an tsaro sun bulla ta wajen.
Wani da ya shaidi lamarin, ya shaida wa Aminiya cewa, a lokacin da ayarin motocin suka bullo, wani babba a cikin tawagar ya fito daga cikin mota tare da neman da a bude masu daya hanyar, amma sai ’yan asalin al’ummar yankin suka ki amincewa da bukatar hakan.
Ya kara da cewa, matasan sun bi motocin ayarin da jifa bayan sun kutsa ta daya hanyar da nufin wucewa, kuma a nan ne sai wasu daga cikin jami’an tsaron suka yi harbi cikin iska, a yayin da wani kuma ya harbi daya daga cikin matasa ’yan asalin yankin mai suna Timothy John, da ya mutu nan take.
Bayan nan, ayarin sun wuce da motocinsu cikin hanzari, kamar yadda aka bayyana wa Aminiya.
A yayin zantawarsa da Aminiya shugaban n ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin adaidaita sahu ya ce, daya daga cikin direbobinsu mai suna Yusuf Auwal na cikin wadanda harsashin bindiga ya bi ta jikinsa.
Ya ce, bayan nan an garzaya da shi zuwa garinsu inda yake cigaba da jinya a yanzu.
Babban Kwamandan Hukumar Kare Hadurra na FRSC mai kula da yankin Dutsen-Alhaji, Mista Luka Wuna, ya tabbatar da faruwan haduran biyun, da kuma rasa rayukan, a yayin zantawarsa da wakilinmu a kan lamari.
Akwai bukatar ilimantar da direbobin Tifa
Binciken Aminiya ya bayyanan cewa, matsalar da tifofi ke samu ta shanyewar burki a yayin da suka ɗauko kaya kuma suka sukwano gangarar da daga ita sai marabar titin ita ce a mafi yawan lokaci ke haddasa munanan hadurra a wannan mahada.
Da yawan direbobin tifa matasa ne da basu san dokokin tuki ba sannan kuma suna tukin da ganganci tamkar suna tuka kananan motoci.
Don haka mafi yawa ba sa kula da yadda suke shawo wannan gangara ta la’akari da cewa, burkin tifa iska ce.
Wani masanin harkokin sufuri da ba ya son a ambaci sunansa ya ba da shaara cewa, ya kamata hukumomin da abin ya shafa su rinka shirya wa direbobin musamman na Tifa bita kan ka’idojin tuki da alamomin hanaya da kuma hatsarin da ke tattare da burkin mota mai dauke da iska.
Abinda ke jawo hatsari a wajen
Malam Anas Mu’azu na cikin ma’aikatan tattara haraji na Karamar Hukumar Bwari da ke ba da tikiti a wajen.
Ya ce, yawancin direbobi da ke fuskantar hatsarin baki ne da ke bi ta gangaren hanyar ba tare da cikakken masaniya a kan yadda wajen yake ba.
Ya ce, ”wutar ba da umarnin wucewa a wajen da ke da kusurwa 4 na bukatar tsayawar mota na wani lokaci a duk ta inda ta fito saboda dogon layi da motoci ke yi, sannan indan wutar ta haska don wucewa, adadi kadan ne na motoci ke iya wucewa kafin ta sake bukatar tsayar da mota,” in ji shi.
Malam Anas ya kara da cewa yawancin bakin direbobi da ke bin hanyar ba su da masaniya a kan tsarin wutar da kuma yanayin hanyar kasancewar babu allunan alamomi na hanya da ke fadakarwa a kan titin.
Ya ce, haka kuma a baya an cire kunyar kan titi da ke sa motoci rage gudun mota. ”A baya akwai kunyar titi na rage gudun da adadinsu ya kai kamar guda biyar, amma sai a ka cire su a lokaci guda ta hanyan kankare su daga kan hanyar,” in ji shi.
Ya ce, ko da Ministan Birnin Abuja Mista Nyesom Wike ya ba da aikin sake gina hanyar a bayabayan nan, ba a maida kunyar titin ba, har zuwa lokacin da haduran baya-bayan nan su ka auku..
Yadda za a magance matsala —Masu Tifa
Haka kuma Aminiya ta zanta da daya daga shugabannin masu motocin tifa da kuma harkar sayar da duwatsu daga kamfanoni biyu na fasa dutsi da ke yankin mai suna Kwamred Ose Idasho inda ya ba da shawarwaari kan yadda ya ke ganin za a magance yawaitar haduran, da ya ce sun bayar a yayin wani zama na musamman da Jami’an Hukumar Magance Hadurra ta FRSC a yankin.
Ya ce, “abu na farko shi ne bukatar a sa alamomin hanya tun daga kamar kilo mita uku kafin mahadar hanyar da zai rika sanar da direba hatsarin wajen tare da bukatar da ya yi takatsantsan.
“Sai kuma a sa abubuwa da ke sa rage gudun mota na kunyar hanya samfurin roba ba na siminta ba, da zai rika yin kara idan direba ya yi yunkurin yin gudu sosai. Hakan zai kara wa direba karsashi ko da ya fara yin gyangyadi.
“Mun kuma bukaci jami’an na FRSC da nemi dauki daga Hukumar Kula da Gine-gine ta Abuja kan su kawar da wuraren da ke sa mutane na tsayawa ta wurin, tare da mayar da shi sarari, sai kuma samar da wurearen yin lodi da kuma hana yin lodi a gefen titin.
“Haka kuma akwai bukatar a gyara wasu daga cikin fitilun ba da hannu da suka daina yin aiki, kamar wanda ya shiga ta bangaren Bamuko ta inda motocin tifa ke shiga da kuma yawan fita.
Sai kuma uwa-uba a gina gadar sama a wajen da zai rage girman gangarowar motoci da ke fitowa ta kusurwar Bwari ko DutsenAlhaji inda motocin za su bi ta saman gada,” in ji jagoran masu motocin tifa.
Ya kamata a gina gadar sama
Shi ma a zantawarsa da Aminiya, Sakataren Hakimin yankin na Dutse-Baupma mai suna Simon Luka da ya yi bayani a madadin hakiminsu, ya ce, hatsarin motoci a wajen ya jima yana jawo masu fargaba da kuma asarar rayuka da dukiya.
Ya buƙaci Ministan Birnin Tarayya Mista Nyesom Wike da ya taimaka wajen yin aikin gadar sama a wajen don magance matsalar.
Ya ce, tarihin farawar matsalar ba za ta gaza shekara 20 bayan an yi aikin hanyar.
Ya ce, matashin da aka kashe bayan jami’an tsaro sun buɗe wuta a wajen mai suna Timothy John, bai wuce shekara 20 ba kuma lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan mai gidansa ya yaye shi daga aikin walda da ya ke yi, inda yake shirin buɗe na kansa.
Ya kara da cewa, “sai dai har zuwa lokacin ziyarar nan babu wata ta’aziyya ko ta jaje da muka samu daga jamiu’an tsaro ko kuma hukuma, kan mutuwar matashin.”
Aminiya ta tuntubi Babbar Jami’ar Hulda da Jama’a a Sakatariyar da ke Kula da Sufuri a yankin Birnin Tarayya Abuja mai suna Misis Lecita Wogu, inda ta buƙaci lokaci don yin tsokaci a kan lamarin.