An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
Published: 6th, April 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun kai hari kan wata motar bas ta sufurin fasinja ta Benue Links da ke kan hanyarta a titin Ikobi na ƙaramar hukumar Otukpo a Jihar Benuwe, inda suka kashe direban da wani fasinja na gaba, yayin da suka yi awon gaba da wasu fasinjojin.
Lamarin ya afku ne da yammacin ranar Alhamis a kusa da rusasshen kamfanin Benue Burnt Bricks, wanda aka fi sani da hanyar shiga garin Otukpo.
Motar mallakar gwamnatin Jihar ta kamfanin Benue Links Nigeria Limited tana kan hanyar Makurdi zuwa Otukpo lokacin da aka yi mata kwanton ɓauna.
A wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na kamfanin, Johnson Ehi Daniel ya fitar a ranar Juma’a, ya tabbatar da faruwar harin, ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro suka mayar da martani cikin gaggawa, tare da bayyana ƙwarin gwiwar ci gaba da ƙoƙarin kuɓutar da fasinjojin da aka sace.
“Benue Links Nigeria Limited ta yi takaicin sanar da harin da aka kai kan wata motar safa mai lamba PP512. Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis, 3 ga watan Afrilu, 2025, kusa da Otukpo Burnt Bricks lokacin da wasu mahara ɗauke da makamai suka yi wa motar kwanton ɓauna.
“Abin takaici, maharan sun harbe direban motar bas mai kujeru 18, Mista Samuel Agege da wani fasinja na gaba, yayin da ’yan bindigar suka yi yunƙurin sace sauran fasinjojin, wasu mutane uku sun yi nasarar tserewa, wani kuma ya sauka tun da farko a garin Taraku kafin faruwar lamarin,” in ji sanarwar.
Hukumomin kamfanin sufurin sun jajantawa iyalan waɗanda suka rasu tare da yin alƙawarin ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro domin ganin an dawo da fasinjojin da aka sace.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da fasinjoji Jihar Benuwe
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
Sun ce suna tafiya daga Yola zuwa Lafia ne lokacin da wasu mutane da ake zargin ‘yan fashi ko masu garkuwa da mutane ne suka kai musu hari, lamarin da ya sa suka tsere zuwa daji don tsira rayukansu.
Sojojin sun taimaka wajen gyara tayar motar sannan suka tabbatar da cewa fasinjojin sun ci gaba da tafiyarsu cikin tsaro.
Shugaban Runduna ta 6, Birgediya Janar Kingsley Uwa, ya yaba wa sojojin bisa saurin ɗaukar mataki da kuma tsayin daka kan aiki.
Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa wajen yaƙi da laifuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp