Francesca Albanze: Abinda Yake Faruwa A Gaza Kisan Kiyashi Ne
Published: 5th, April 2025 GMT
Wakiliyar musamman ta MDD akan Falasdinu Francesca Albanze ta sanar da cewa; Bayanan da jaridar ” New York Times” masu kunshe da hotuna na laifin kashe masu aikin ceto a Rafah, suna dakile riwayar Isra’ila.”
Wakiliyar ta MDD ta fada wa tashar talabijin din Aljazeera cewa, abindaya faru kisan kiyashi ne’ sannan ta kara da cewa sojojin Isra’ilan suna yin abinda suke yi ne a tsare,kuma duniya ta yi shiru.
Jaridar “New York Times” ta watsa faifen bidiyo dake dauke da muryar wani ma’aikacin agaji wanda daya ne daga cikin wadanda aka sami gawawwakinsu a cikin wani babban kabari a yankin Rafaha. Bidiyon ya nuna yadda sojojin Isra’ila su ka kai wa masu aikin agaji hari da gangan, sun kuma san cewa su ne saboda alamomin da suke tattare da su.
Riwayar da HKI ta watsa ita ce, cewa motocin masu aikin agajin sun nufi inda sojojinsu suke ne gadan-gadan cikin shakku.”
Wakiliyar MDD ta kuma kara da cewa; wannan laifin da HKI ta tafka bai kamata a kalle shi nesa da sauran laifukan da take aikatawa ba a Gaza, tana mai kara da cewa; Tun 2023 take yi wa al’ummar Gaza kisan kiyashi a tsare.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
Ministan tsaro na kasar Iran ya bayyana cewa sojojin kasar sun yi gwajin wani makami mai linzami wanda yake iya daukar abubuwan fashewa hart un biyu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Burgediya Janar Amir Nasirzade yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa . wannan gwajin sako ne ga gwamnatin Amurka da kawayenta. Idan wani ya dora mana yaki sai sun fi mu shan wahali. Don tare da wadannan shirye shiryen da kuke na kare kammu sai mun kori amurka daga yankin nan.
Yace iran tana cikin fushi kan abinda yake faruwa a Gaza don haka duk wata dama da ta samu zata maida martanin da ya dace. Ministan ya bayyana haka ne a jiya Laraba bayan taron Majalisar ministoci tare da shugaban kasa.