Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
Published: 22nd, March 2025 GMT
Kasashen Iran da Hadaddiyar Daular Larabawa sun bayyana matukar damuwarsu kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sake dawo da yakin kisan kare dangi a zirin Gaza da kuma hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen.
A wata tattaunawa ta wayar tarho a wannan Juma’a, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da takwaransa na UAE Abdullah bin Zayed Al Nahyan, sun tattauna batutuwan da suka shafi yankin, musamman ma ayyukan wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma hare-haren Amurka a Yemen.
Araghchi ya yi kakkausar suka kan kisan gillar da gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta yi wa daruruwan Falasdinawa da ba su ji ba ba su gani ba tun daga ranar Talata, yana mai jaddada cewa yin hakan saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta ne da aka rattaba hannu a kansa.
Ya kuma yi Allah wadai da hare-haren da sojojin Amurka ke ci gaba da kai wa kasar Yemen, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mata da kananan yara da dama, tare da lalata muhimman ababen more rayuwa na yankin, da kuma jefa mutane cikin kangin talauci da yunwa.
Araghchi ya kara da cewa, laifuffukan da gwamnatin yahudawan sahyoniya ke aikatawa a Gaza da kuma harin da Amurka ta kai kan kasar Yaman na bukatar daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa daga kasashen yankin da kum akasashen musulmi, domin dakatar da wannan ta’addanci da ke ci gaba da kawo rashin tsaro a duk fadin yankin gabas ta tsakiya.
A nasa bangaren, Ministan kasar UAE Abdullah bin Zayed ya bayyana matukar damuwarsa kan tabarbarewar al’amura a yankin, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa matuka.
Ya jaddada bukatar ci gaba da tuntubar juna tsakanin kasashen yankin domin hana ci gaba da tabarbarewar zaman lafiya.
Rahotanni sun tabbatar da cewa sojojin Isra’ila sun zafafa kai hare-hare ta sama da kuma ta kasa a zirin Gaza tun daga ranar Talata, inda suke kai hari kan wuraren zaman jama’a da hakan ya hada da wuraren da aka tsugunnar da dubban mutane da suka rasa muhallansu da kuma gidaje, gami da asibitoci, tare da hana duk wasu ayyuka na jin kai ko ceton jama’a ko kai daukin gaggawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
Sojojin kasar Iran sun cilla makamai masu linzami da kuma jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan HKI a dazuda nan nan, wayo yau lahadi a ci gaba da musayar wauta da suke yi da sojojin HKI kwanaki uku da suka gabata.
Kamfanin dillancin labaran kare kai na kasar Iran Tasnim ya nakalto sojojin kasar na cewa sun cilla makamai masu linzami da Drones a karon farko da rana ido na ganin ido a kan HKI kuma tuna makaman sun fada a inda yakamata su fada a cikin haramtacciyar kasar.
A safiyar ranar jumma’a ce sojojin HKI suka kai hare-hare kan birnin Tehran inda suka kai manya-manyan jami’an sojojin kasar ga shahada, sannan suka kashe mutane fararen hula wadanda basu da laifi.
Bayan haka ne sojojin JMI suka fara maida martani a daren Asabar da daren lahadi, amma a wannan karon sun kai hare haren ne da ranar Lahadi ido na ganin ido.
Hare-haren wadanda aka basu suna “Alkawalin gaskiya Na 3 zasu ci gaba matakar HKI ta ci gaba da kaiwa Iran hare hare.