Aminiya:
2025-06-15@08:05:45 GMT

Mun ceto Najeriya daga faɗa wa mummunan yanayi — Tinubu

Published: 14th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce da tuni Najeriya ta faɗa cikin mummunan yanayin matsin tattalin arziƙi ban da gwamnatinsa ta ɗauki matakan da suka dace a kan lokaci.

Da yake jawabi a fadar gwamnati da ke Abuja, Tinubu ya bayyana wa wata tawagar tsofaffin ’yan majalisa cewa dole ne gwamnatinsa ta ɗauki matakai domin tabbatar da kyakkyawan makoma ga ƙasar.

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Kano: Gobara ta kashe mutum 7 da lalata kadarorin N50m a Fabrairu

“Tsawon shekaru 50, Najeriya na kashe kuɗin ’ya’yanmu wajen samar da man fetur ga maƙwabtan ƙasashe. Dole ce ta sa muka tsara makomar yaranmu,” in ji shi.

Shugaban ya amince da cewa ana fuskantar ƙalubale a fannin tattalin arziƙi tun farkon mulkinsa, amma ya jaddada cewa matakan da aka ɗauka suna da muhimmanci.

“Muna cikin mawuyacin hali lokacin da na karɓi mulki. Idan ba mu ɗauki matakan da suka dace ba, tattalin arziƙin Najeriya zai durƙushe,” in ji Tinubu.

Ya kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa abubuwa na ƙara gyaruwa, “A yau, muna kan turbar da ta dace. Farashin canjin kuɗi yana daidaituwa, farashin abinci yana raguwa, musamman a lokacin azumin Ramadan. Akwai nasara a tafiyar.”

Sanata Emmanuel Chiedoziem Nwaka, wanda ya jagoranci tawagar, ya yaba wa matakan Tinubu, musamman shirin bai wa ɗalibai rance domin tallafa wa iliminsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Tattalin Arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Da yake magana kan muhimmancin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana, Idris ya ce wannan ba lokacin murna kaɗai ba ne, har ma lokaci ne na nazari kan cigaban ƙasar wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da farfaɗowar tattalin arziki.

 

Ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka tara daga cire tallafin man fetur wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ciki har da manyan tituna guda biyu da za su haura kilomita 1,700, waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci da haɗa yankuna daban-daban.

 

Ya ce: “Manufar ba wai haɗa yankuna ba ce kawai, amma samar da damarmakin tattalin arziki.

 

“Nijeriya na ƙoƙarin komawa kan sahihiyar hanyar ta. Tana sake zama ƙasa mai daraja a idon duniya.

 

“Martabar da Nijeriya ke da ita a baya tana dawowa sannu a hankali. Masu zuba jari suna samun ƙarin ƙwarin gwiwa a ƙasar.”

 

Ya ƙara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata sun wuce batun tattalin arziki kawai, domin suna gina tushe ne na cigaba mai ɗorewa, raba dama ga kowa, da ƙarfafa gaskiya da riƙon amana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa