Aminiya:
2025-08-01@01:41:23 GMT

Mun ceto Najeriya daga faɗa wa mummunan yanayi — Tinubu

Published: 14th, March 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce da tuni Najeriya ta faɗa cikin mummunan yanayin matsin tattalin arziƙi ban da gwamnatinsa ta ɗauki matakan da suka dace a kan lokaci.

Da yake jawabi a fadar gwamnati da ke Abuja, Tinubu ya bayyana wa wata tawagar tsofaffin ’yan majalisa cewa dole ne gwamnatinsa ta ɗauki matakai domin tabbatar da kyakkyawan makoma ga ƙasar.

Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Kano: Gobara ta kashe mutum 7 da lalata kadarorin N50m a Fabrairu

“Tsawon shekaru 50, Najeriya na kashe kuɗin ’ya’yanmu wajen samar da man fetur ga maƙwabtan ƙasashe. Dole ce ta sa muka tsara makomar yaranmu,” in ji shi.

Shugaban ya amince da cewa ana fuskantar ƙalubale a fannin tattalin arziƙi tun farkon mulkinsa, amma ya jaddada cewa matakan da aka ɗauka suna da muhimmanci.

“Muna cikin mawuyacin hali lokacin da na karɓi mulki. Idan ba mu ɗauki matakan da suka dace ba, tattalin arziƙin Najeriya zai durƙushe,” in ji Tinubu.

Ya kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa abubuwa na ƙara gyaruwa, “A yau, muna kan turbar da ta dace. Farashin canjin kuɗi yana daidaituwa, farashin abinci yana raguwa, musamman a lokacin azumin Ramadan. Akwai nasara a tafiyar.”

Sanata Emmanuel Chiedoziem Nwaka, wanda ya jagoranci tawagar, ya yaba wa matakan Tinubu, musamman shirin bai wa ɗalibai rance domin tallafa wa iliminsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Tattalin Arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam

Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa’adin da ya kamata ya yi na shugabancin hukumar.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

A cewarsa, wa’adin Mista Adeniyi zai ƙare ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025.

Amma yanzu Shugaba Tinubu ya amince da ƙara masa shekara ɗaya, wanda hakan ke nufin zai ci gaba da zama a kan kujerarsa har zuwa watan Agustan 2026.

Sanarwar ta bayyana cewa ƙarin wa’adin zai ba shi damar kammala wasu muhimman ayyuka da yake yi.

Waɗannan ayyukan sun haɗa da gyara da inganta harkokin Kwastam, kammala wani shiri da zai sauƙaƙa kasuwanci a Najeriya, da kuma taimaka wa ƙasar wajen cika alƙawuran da ta ɗauka ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu, ya yaba da ƙwazon Mista Adeniyi da yadda yake gudanar da ayyukansa.

Ya ce ƙarin wannan wa’adin zai taimaka wajen inganta hanyoyin tara kuɗaɗen shiga a hukumar, da kuma tabbatar da tsaro a iyakokin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata