Wata Rana Za A Yi Wa Gwamnatin Tinubu Sambarka – Minista
Published: 14th, March 2025 GMT
Ya ce: “Bari in ce mun tsallake tudu, kuma wahalhalun da aka sha a baya suna raguwa yayin da tasirin waɗannan sauye-sauye suke fara bayyana.
“A halin yanzu, muna gani muraran yadda farashin kayan abinci yake saukowa, farashin musayar kuɗaɗe yake daidaituwa, kuma farashin man fetur yana raguwa. Waɗannan duk alamu ne cewa ayyukan garambawul da ake aiwatarwa suna haifar da sakamako mai kyau.
Ministan ya bayyana cewa sauye-sauyen da suke da ma’ana ba su zuwa da sauƙi, domin suna buƙatar haƙuri, juriya, da kuma sadaukarwa don cimma cigaba mai ɗorewa.
“Ƙasar mu tana kan wani muhimmin mataki yayin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yake aiwatar da sauye-sauye masu ƙarfi domin gina sabuwar Nijeriya. Tarihi ya nuna cewa sauye-sauyen da ke kawo cigaba ba su da sauƙi; suna buƙatar sadaukarwa, haƙuri, da jajircewa wajen cimma cigaban da zai ɗore.
“Wahalhalun farko da ke tattare da waɗannan sauye-sauye wasu abubuwa ne waɗanda dole ne a fuskance su domin samun cigaba mai ɗorewa.
“Ina matuƙar gode wa ‘yan Nijeriya bisa haƙurin su, juriya, da kuma cikakken imani da hangen nesa na Shugaban Ƙasa,” inji shi.
Idris ya kuma buƙaci shugabannin addinai da su yi amfani da lokutan azumin Ramadan da Lent wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya, da tsaro, da cigaban ƙasa.
“Ina kira ga shugabannin Musulmi da Kirista, musamman a wannan lokaci na azumi da tunani mai zurfi, da su ci gaba da yin addu’a domin samun nasarar Nijeriya.
“Tare da haɗin kai, imani, da ƙoƙari tare, za mu fito da ƙarfi, da juriya, kuma mu kasance a cikin matsayi mafi kyau don samun cigaban da zai ɗore.”
Taron ya samu halartar Ministan Sufurin Jiragen Sama da Kawo Cigaba a Fannin Sararin Samaniya, Mista Festus Keyamo, da Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, waɗanda suka bayyana nasarorin da ma’aikatun su suka samu zuwa yanzu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
Ya ce kuma kayan da ake fitarwa zuwa waje waɗanda ba man fetur yanzu su kusa yin kai da kai da fetur.
Ya ƙara da cewa ajiyar kuɗaɗen ƙasar a waje ya haura kusan dala biliyan 42, daga biliyan 32 lokacin da Tinubu ya hau mulki.
Har ila yau, ya ce an biya bashin da ya haura biliyan bakwai, ciki har da miliyan 800 da ake bin jiragen saman Nijeriya.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yanzu jihohi na iya biyan albashi da fansho a kan lokaci, sannan suna da rarar kuɗi don ayyukan raya ƙasa, abin da ba a saba gani ba a baya.
“Bayan shekara biyu da watanni biyar kacal a ofis, Shugaba Tinubu ya cimma abubuwa da dama. Ko da Atiku da magoya bayansa ba su yadda ba, ’yan Nijeriya suna ganin sauyin,” in ji Onanuga.
Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma zargi Atiku da jam’iyyar PDP da yaɗa maganganun da za su kawo tashin hankali.
Ya bayyana cewa yawancin matsalolin da ake fuskanta sun samo asali ne daga rashin kyakkyawan shugabanci tun a lokacin PDP, lokacin da Atiku yake mataimakin shugaban ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp