’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno
Published: 1st, December 2025 GMT
’Yan sanda sun gano tare da miƙa wa wata mata zinarenta da kuɗinsu ya kai Naira miliyan 23 da suna ɓace a lokacin wani harin Boko Haram shekara 13 da suka gabata a Jihar Borno.
Jami’an tsaro da ke sintiri a kan iyakar Jihar Borno da Nijar ne suka gano kayan zinaren da suka ɓace tuna shakarar 2012, waɗanda suka haɗa da sarƙoƙi da sulallan zinariya a yankin Ƙaramar Hukumar Abadam.
Jami’an Ƙaramar Hukumar ne suka sanar a ranar Asabar a Malam Fatori cewa tsabar zinaren da aka gano, darajarsu ta kai Naira miliyan 23, mallakin wata uwa ce mai ’ya’ya shida.
Matar, wacce ke zaune a gaɓar Tafkin Chadi, ta ce, “A yau ina cike da farin ciki game da gano tsabar zinare na masu daraja da suka ɓace tun 2012, lokacin da ’yan Boko Haram suka ƙona gidaje da shaguna da yawa a cikin al’ummarmu.”
Ta jaddada cewa, “babu daga cikin zinare da aka samu ya ɓace ko ya lalace a lokacin mamayar Malam Fatori da ’yan ta’adda suka yi fiye da nawa.”
Wani babban jami’in Majalisar Ƙaramar Hukumar Abadam da ya sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya yaba wa ’yan sandan da aka tura don kare rayukan mutane da kadarorinsu a yankin Tafkin Chadi.
Bayan gano tsabar zinare na naira miliyan 23, jami’in ya lura cewa martanin ’yan sanda a ayyukan yaƙi da ta’addanci da ake ci gaba da yi wani abin karfafa gwiwa ne ga sojoji da sauran hukumomin tsaro a yankin Tafkin Chadi, wanda ya ƙunshi qananan hukumomi takwas da ke yankin.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce Najeriya na buƙatar taimakon ƙasashen waje don dakatar da kashe-kashe da rashin tsaro, domin gwamnati ta gaza kare al’umma.
Ya bayyana haka ne a wani taro da ya gudana Jihar Filato, inda ya ce a ci gaba ya kawo fasahar da za a iya gano masu aikata laifi, amma ta gaza yin hakan.
Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a KanoObasanjo, ya yi gargaɗin cewa ana kashe ’yan Najeriya ba tare da la’akari da addini ko ƙabilanci ba, don haka gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki.
Ya ce idan gwamnati ta kasa kare jama’a, ’yan ƙasa na da damar neman taimakon ƙasashen duniya.
Ya soki masu kare kashe-kashen da ake yi, inda ya bayyana cewa rayuwar kowanne ɗan Najeriya na da muhimmanci.
Obasanjo, ya kuma tambayi dalilin da ya sa gwamnati ke tattaunawa ko biyan kuɗin ’yan bindiga kuɗin fansa, inda ya ce hakan na ƙara taɓarɓarewar lamarin.
Ya kira ’yan Najeriya da su haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya, tare da tabbatar da cewa kowa na rayuwa ba tare da fargaba ba.
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, shi ma ya yi jawabi a wajen taron.
Ya ce al’ummar jihar dole su haɗa kai su daina abubuwan da za su raba su.
Mutfwang, ya buƙaci jama’a su yi aiki tare domin jihar ta ci gaba da kuma shawo kan matsalolin tsaro.