A Gobe Litinin Za A Yi Atisayen Sojan Ruwa Na Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashen Iran, Rasha Da China
Published: 9th, March 2025 GMT
Kamfanin dillancin labarun “ Irna” ya nakalto cewa; Jiragen ruwa na soja da kuma dakarun kare juyin musuluni na Iran za su shiga cikin atisayen na hadin gwiwa da kasashen Rasha da kuma China.
Bugu da kari da akwai wasu kasashen da za su turo sojojin masu sa ido, da su ne; jamhuriyar Azerbaijan, Afirka Ta Kudu, Oman, Khazakistan da Pakistan.
Wannan atisayen dai za a yi ne a sansani na uku na sojan ruwan Iran wanda yake a arewacin tekun Indiya.
Manufar wannan atisayen dai shi ne bunkasa yadda kasashen za su rika aiki tare a tsakanin kasashen sojojin ruwan Iran, Rasha da kuma China.
Wannan dai ba shi ne karon farko da sojojin ruwan kasashen Iran Rasha da kuma China su ka yi atisayen soja na hadin gwiwa ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.
Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.
Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.