Kamfanin dillancin labarun “ Irna” ya nakalto cewa; Jiragen ruwa na soja da kuma dakarun kare juyin musuluni na Iran za su shiga cikin atisayen na hadin gwiwa da kasashen Rasha da kuma China.

Bugu da kari da akwai wasu kasashen da za su turo sojojin masu sa ido, da su ne; jamhuriyar Azerbaijan, Afirka Ta Kudu, Oman, Khazakistan da Pakistan.

Sai kuma kasashen Katar, Iraki, HDL da kuma Srilanka.

Wannan atisayen dai za a yi ne a sansani na uku na sojan ruwan Iran wanda yake a arewacin tekun Indiya.

Manufar wannan atisayen dai shi ne  bunkasa yadda kasashen za su rika aiki tare a tsakanin kasashen sojojin ruwan Iran, Rasha da kuma China.

Wannan dai ba shi ne karon farko da sojojin ruwan kasashen Iran Rasha da kuma China su ka yi atisayen soja na hadin gwiwa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kokarin Kasar Sin Na Bunkasa Hadin Gwiwar Neman Ci Gaban Duniya Na Nan Daram

Kakakin hukumar raya hadin gwiwar neman ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin (CIDCA), Li Ming, ya bayyana a gun taron manema labaru na yau Litinin cewa, rage yawan tallafin kasashen waje da Amurka ta yi, da rage fiye da kashi 90 cikin 100 na ayyukan da take yi, sun sabawa alkawuran da ta dauka, da kuma nauyin da ke bisa wuyanta a karkashin tsarin MDD, kuma hakan wani yunkuri ne na ja da baya, wanda kasashen duniya ba sa goyon baya.

Li Ming ya jaddada cewa, alkawarin da kasar Sin ta yi na kara yawan albarkatu ga hadin gwiwar ci gaban duniya, ba zai canza ba. Ya kara da cewa, ka’idojin kasar Sin na kin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu, da kin sanya sharadi na siyasa, da kin yin alkawuran banza suna nan daram. Ban da wannan kuma, yadda kasar Sin ke bin tsarin ba da tallafi na ketare bisa gaskiya da rikon amana, da kudurinta na yin shawarwari bisa daidaito da hadin gwiwar samun nasara tare da kasashe masu ci gaba da masu tasowa ba za su canza ba.

Li Ming ya ci gaba da cewa, dole ne kasashen da suka ci gaba su tabbatar da bin ra’ayin bangarori daban daban bisa gaskiya, da mutunta alkawuransu na tabbatar da ci gaba, da nuna sanin ya kamata, da yin watsi da dabarun tashin wani faduwar wani, da hada kai da kasashe masu tasowa, don ci gaba da aiwatar da ajandar ci gaba mai dorewa ta MDD ta shekarar 2030, da gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
  • Nijar, Burkina Faso da Mali sun fice daga kungiyar kasashe renon Faransa
  • Yemen Ta Cilla Makamai Kan Kataparen Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Yaki Na Amurka A Tekun Red Sea
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da Faransanci
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da da Faransanci
  • Kokarin Kasar Sin Na Bunkasa Hadin Gwiwar Neman Ci Gaban Duniya Na Nan Daram
  • Atisayen Soji A Mashigin Tekun Taiwan Babban Gargadi Ne Ga ‘Yan Awaren Taiwan
  • MDD ta bukaci masu ruwa da tsaki a Yemen da su kai zuciya nesa
  • Iran ta kuduri aniyar yin hadin gwiwa da hukumar IAEA