Aminiya:
2025-12-13@12:36:37 GMT

Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro

Published: 3rd, December 2025 GMT

Majalisar Dattawan Najeriya za ta tantance wanda Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa a matsayin Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, a zamanta na yau Laraba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa daga ofishin Shugaban Masu Rinjaye na majalisar, Opeyemi Bamidele.

Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro

Sanarwar ta ce majalisar ta karɓi buƙatar Shugaban Ƙasa Tinubu na tabbatar da wanda aka naɗa Ministan Tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa za a karanta wasikar a gaban majalisar a ranar Laraba, sannan kuma za a ci gaba da tantance wanda aka naɗa nan take.

Opeyemi ya bayyana cewa majalisar ba za ta iya jinkirta irin wannan buƙata ba a wannan lokaci mai muhimmanci, domin ta shafi muhimman abubuwan da suka shafi ƙasar.

A ranar Talat ace Tinubu ya aike da sunan Christopher gaban majalisar domin amincewa bayan murabus din tsohon Ministan, Muhammad Bdaru Abubakar.

Kafin nadin nasa dai, Christopher shi ne tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya da Tinubu ya sauke tare da ragowar manyan hafsoshi a kwanakin baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majlisar Dattawa Ministan Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’

Ministan Harkokin Waje na Jamhuriyar Benin, Olushegun Adjadi Bakari, ya ce kimanin sojoji 200 daga Najeriya da Ivory Coast yanzu haka na cikin kasar shi a matsayin wani ɓangare na aikin tsaro don tallafa wa gwamnati.

Ƙaramar ƙasa ta Yammacin Afirka ta girgiza da yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a ranar Lahadi, wanda ya sa Najeriya, Faransa da Ivory Coast suka tashi tsaye wajen goyon bayan gwamnatin farar hula.

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota

“A halin yanzu akwai kusan sojoji 200 da suka zo don ba da taimako ga rundunar tsaron Benin a cikin aikin sharewa da tsaftacewa,” in ji Olushegun Adjadi Bakari ga ’yan jarida a taron manema labarai da aka yi a Abuja ranar Alhamis.

Wata majiyar tsaro daga Ivory Coast ta ce Abidjan ta turo sojoji 50 a matsayin ɓangare na wannan aiki, inda ƙungiyar ECOWAS ta bayyana cewa za a haɗa da sojoji daga Ghana da Saliyo.

Najeriya ta ce sojojinta sun isa Benin tun ranar Lahadi. ECOWAS ba ta bayyana adadin sojojin da ake sa ran za su shiga ba.

Bakari ya ce lokacin da rundunar Benin ta nemi taimako, shirin juyin mulkin “ya riga ya yi wargaje.”

Ya ce sojojin Benin masu biyayya sun fatattaki harin farko, amma lamarin na buƙatar kulawa sosai don kauce wa asarar rayukan fararen hula.

“Mun nemi goyon bayan ’yan’uwa ba saboda rundunarmu ba za ta iya ba, amma saboda Shugaban Ƙasa bai so a yi asarar rayuka masu yawa ba.”

Ya ƙara da cewa kai hari kai tsaye zuwa sansanin masu juyin mulkin na iya haifar da zubar da jini mai yawa. “Shi ya sa Shugaba Patrice Talon ya nemi goyon bayan Jamhuriyar Tarayyar Najeriya.

“Rundunar Benin ta yi nasarar fatattakar wannan yunƙurin juyin mulki, amma haɗarin asarar rayuka da dama ya sa aka buƙaci martani na haɗin gwiwa.”

Ana ci gaba da tattaunawa kan ko sojojin tsaro na yankin za su ci gaba da zama na ɗan lokaci, amma Bakari ya ce duk wani mataki “za a ɗauka ne tare da haɗin gwiwar rundunar tsaro ta Benin, wadda ta nuna jarumta.”

Yadda Najeriya ta taimaka wa Benin — Tuggar

A taron ministocin ECOWAS da aka yi a Abuja, Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya ce saurin matakan diflomasiyya, na soja da na leƙen asiri tsakanin Najeriya da Benin ne ya taimaka wajen dakile juyin mulkin.

Tuggar ya ce lamarin ya nuna yadda za a iya kare dimokuraɗiyya idan ƙasashe makwabta suna sadarwa yadda ya kamata.

Ya ce, “Haɗin kai don tabbatar da cewa dimokuraɗiyya ta ci gaba da kasancewa a Benin ya yi nasara, kuma wannan misali ne na abin da ya kamata a yi duk lokacin da dimokuraɗiyya ke fuskantar barazana a yankinmu.”

A halin yanzu, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa Pascal Tigri, wanda ake zargi da jagorantar juyin mulkin da bai yi nasara va, tare da abokan aikinsa suna buya a Togo.

A ranar Laraba, jami’an gwamnatin Benin suka shaida wa Reuters cewa shugaban juyin mulkin yana gudun hijira a Lome 2, unguwa a babban birnin Togo inda gidan shugaban ƙasar, Faure Gnassingbe yake.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • NAJERIYA A YAU: Alfanu Da Kalubalen Sabon Jadawalin Karatun Makarantu Da Gwamnati Ta Bijiro Dashi
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro