NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
Published: 2nd, December 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Cutar kansar mama na ɗaya daga cikin manyan cututtukan da ke addabar mata a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
An kiyasta cewa mata sama da dubu ɗari biyu na kamuwa da cutar a kowace shekara a Najeriya, yayin da miliyoyin mata a duniya ke fama da wannan cuta. Abin damuwa shi ne cewa yawancin lokuta ana gano cutar ne a kurarren lokaci, wanda hakan ke sa magani ya yi wahala kuma ya rage yiwuwar ceto rayuwar wanda ya kamu da shi.
Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gidauniyar yaki da cutar kansa kansar mama
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Janar Christopher CG Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa a Fadar Shugaban Kasa.
Ganawar Tinubu da Janar CG Musa ya auku ne a ranar Litinin da dare, jim kadan kafin sanarwar murabus din Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.
Majiyoyi na cewa gananawar shugaban kasa da Janar CG Musa na da nasaba da shirin shugaban kasar na cike gurbin da Badaru ya bari da kuma garambawul a shugabancin tsaron Najeriya.
Mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanar cewa Badaru ya yi murabus ne saboda dalilai na rashin lafiya.
An kama ’yan bindiga 4 a Kano MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’arBadaru ya ajiye aiki ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da karuwar matsalar tsaro musammana a shiyyar Arewa lamarin da ya sa Shugaba Tinubu ya ayyan dokar ta-baci kan sha’anin tsaro.
A cikin ’yan watannin nan ’yan ta’adda a hare-harensu, suka kashe wani Janar din soja, Kwamandan Birget na 25 da ke Jihar Borno, Birgediya-Janar Uba Musa da dakarunsa a Jihar Borno, inda kuma suka yi garkuwa da wasu mata a gona.
A kwanan nan ’yan ta’adda sun tsananta kai hare-hare a Jihar Kano, baya ga sace daruruwan dalibai a jihohin Kebbi da Neja da kuma yin garkuwa da masu ibada a Jihohin Kwara da Kogi da kuma sace wasu mata a Borno.