’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
Published: 6th, December 2025 GMT
An harbe wani jami’in ɗan sanda har lahira, yayin da yake tsaka da binciken ababen hawa a Benin a Jihar Edo.
Kakakin rundunar, CSP Moses Yamu, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 12 na ranar Juma’a, lokacin da jami’an rundunar suka tsayar da wata baƙar mota ƙirar Lexus, amma ta ƙi tsayawa.
’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno Ƙasashen waje na taimaka wa ’yan ta’adda a Najeriya —Sheikh GumiƊaya daga cikin mutanen da ke cikin motar ya buɗe wa jami’an da ke shingen wuta, sannan suka tsere.
A dalilin haka ne suka harbe wani ɗan sanda wanda ba a bayyana sunansa ba har lahira.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Monday Agbonika, ya umarci a farauto waɗanda suka aikata laifin.
Ya roƙi jama’a su bayar da sahihan bayanai, musamman idan suka ga irin wannan motar da aka zayyana.
Rundunar ta tabbatar wa jama’a cewa an ƙara tsaurara tsaro a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Ɗan Sanda hari
এছাড়াও পড়ুন:
NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
Hukumar Hana Safarar Mutane (NAPTIP) shiyyar Kano, ta kama wani mutum da ya yi yunƙurin safarar wasu mata bakwai zuwa Saudiyya.
Jami’an NAPTIP sun kai samame wani gida a Kano a ranar 2 ga watan Nuwamba, 2025, bayan samun bayanan sirri, inda aka ɓoye matan da ake shirin safararsu.
Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan TsaroA cewar Mohammed Habib, Jami’in Hulɗa da Jama’a na NAPTIP a Kano, an ajiye matan a gidan ne yayin da ake shirin tura su Saudiyya domin yin aikatau.
Ya ce, “Bincike ya nuna cewa biyu daga cikin waɗanda aka ceto ’yan Nijar ne, yayin da biyar kuma ’yan Najeriya ne.”
Ya ƙara da cewa, “An kai matan Accra a Ghana, inda aka yi musu biza. Kuma duka aikin da za a musu bashi ne, inda kowacce za ta biya Naira miliyan 10, idan sun yi aikin wahala a Saudiyya .”
NAPTIP ta bayyana cewa an riga an kammala shirin tura matan filin jirgin saman Abuja a ranar 3 ga watan Disamba, 2025, wanda a nan aka shirya tafiyarsu Saudiyya.
Hukumar ta ce an kama mutum ɗaya, yayin da sauran waɗanda ke da hannu a lamarin suka tsere.
Jami’in, ya tabbatar da cewa hukumar na ci gaba da bincike domin kama sauran da suka tsere.