Aminiya:
2025-12-05@06:28:03 GMT

An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi

Published: 5th, December 2025 GMT

Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasa ransa bayan fada ya barke a lokacin bikin radin suna a ƙauyen Kwata da ke Karamar Hukumar Warji ta Jihar Bauchi.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da sa’insa ta barke tsakanin wasu matasa ta rikide ta zama fada, wanda ya bar Haruna cikin rashin hayyacinsa.

Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

“Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna na ƙauyen Kwata, Karamar Hukumar Warji, Jihar Bauchi, ya riga mu gidan gaskiya bayan rikici mai tsanani da ya barke a bikin radin suna a ranar 2 ga watan Disamba, 2025,” in ji Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro a yankin arewa maso gabas.

Ya kara da cewa rashin jituwa tsakanin wasu matasa a wajen bikin ta rikide zuwa fada, lamarin da ya bar wanda abin ya shafa ya suma nan take.

An ce an garzaya da Haruna zuwa Asibitin Gwamnati na Warji, amma ya rasu a yayin da ake masa jinya.

Da aka tuntubi mai magana da yawun ’yan sanda na jihar, Ahmed Wakili, ya ce yana cikin taro kuma ya yi alƙawarin dawowa da bayani, sai dai bai yi hakan ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: radin suna

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa

Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta kama matashin nan da ake zargi da kashe makwabciyarsa a unguwar Shuwari II, a garin Maiduguri babban birnin jihar, ta hanyar daba mata wuka.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na dare a ranar Talata.

Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa

Ya ce ana zargin matashin ne mai shekaru 17 da aka fi sani da Amir, wanda makanike ne da kashe matar ta hanyar daba mata wuka.

Wani makwabcin wajen ya shaida cewa ana zargin matashin ne da shiga gidan ta hanyar tsallake katanga bayan ya jira ragowar mutanen gidan sun shiga ciki.

A cewar majiyar, matashin ya ɗauki wuƙa ya daba wa matar gidan, wadda ba a bayyana sunanta ba, a ƙirji da wuya, sannan ya tafi da wayarta da na’urar cajin hannu (power bank).

Majiyar ta ƙara da cewa bayan aikata laifin, wanda ake zargin ya koma gidansu ya wanke tufafinsa da kayan da ya yi amfani da su domin kauce wa bin sahunsa.

Rahotanni sun ce ƙanwar mijin wadda aka kashe ce ta fara sanar da jama’a bayan ta ji ihun matar tana neman taimako.

Lokacin da ta fito ta duba, sai ta ga wanda ake zargin yana gudu ya koma gidansu.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa jami’an ’yan sanda sun kama matashin da misalin ƙarfe 2:30 na rana.

Sai dai kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, bai samu damar yin ƙarin bayani ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi
  • ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa
  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran