Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
Published: 5th, December 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, tare da haɗin gwiwar maharba, sun samu nasarar tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da aikata laifuka a Jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da Adamawa.
Rundunar ta samu nasarar ne bayan kama Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40 daga ƙauyen Tilde a Funakaye, a ranar 23 ga watan Nuwamba 2025.
An kama shi ne bayan samun bayanan sirri kan hulɗa da masu satar shanu.
Abdullahi, ya amsa cewa yana da hannu a garkuwa da mutane tare da bayyana sunayen waɗanda suke aikata laifin tare.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, jami’an Operation Hattara tare da maharba ne suka kai samame maɓoyarsu a ranar 28 ga watan Nuwamba 2025, inda suka kama mutum shida bayan yin artabu.
Waɗanda aka kama sun haɗa da; Usman Mohammed, Hussain Idris, Adamu Tukur, Ya’u Abdullahi, Ali Umar, Hassan Usman da Abdullahi Ibrahim.
Rundunar ta ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa suna da hannu a garkuwa da mutane tare karɓar kuɗin fansa kusan Naira miliyan 150.
Jami’an sun shiga dajin Gadam, inda suka samu bindiga ƙirar GPMG mai jigida guda ɗaya da harsasai takwas bayan wata musayar wuta da suka yi wasu ’yan ta’adda da suka tsere.
Haka kuma an gano suna da hannu wajen garkuwa da wani mutum a ƙauyen Barderi a Akko, a ranar 15 ga watan Janairun 2025.
Sun tsare mutumin na tsawon makonni biyu kafin karɓar Naira miliyan 15 a matsayin kuɗin fansa.
DSP Buhari, ya ce ana cigaba da bincike, kuma za a gurfanar da su a kotu.
Ya roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin inganta harkokin tsaro.
Rundunar ‘Yan Sandan Gombe ta ce za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda garkuwa da mutane maharba garkuwa da mutane
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya ce ba zai bai wa ’yan Najeriya kunya ba, saboda ƙwarin guiwar da suke da shi a kansa.
Musa, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa ministan tsaro, ya bayyana haka ne a ranar Laraba lokacin da aka tantance shi a Majalisar Dattawa.
Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyuYa gode wa Shugaban Ƙasa saboda zaɓarsa da ya yi a matsayin minista, sannan ya gode wa ’yan Najeriya saboda amincewa da suka yi da shi.
Ya yi alƙawarin yin iya bakin ƙoƙarinsa domin tabbatar da zaman lafiya a ƙasar nan.
Ya ce: “Da na ga irin martanin mutane bayan an ambaci sunana, na san cewa ba zan bari na gaza ba, ba zan bai wa ’yan ƙasata kunya ba. Duk abin da ya kamata mu yi, za mu yi, kuma na san da taimakon Allah za mu yi nasara.”
Musa ya ƙara da cewa abin ya ba shi mamaki ganin irin goyon bayan da aka ba shi a kafafen sada zumunta.
“Na je kafafen sada zumunta kuma abin ya ba ni mamaki ganin irin martanin mutane. Wannan yana nuna cewa mutane suna son ganin Najeriya ta zauna lafiya.”
Ya ce wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son Najeriya, amma bai yadda da wannan batu ba.
“Idan wasu suna cewa ’yan Najeriya ba sa son ƙasarsu ina cewa ba haka abun yake ba, ba su san ’yan Najeriya ba.”
Ya kuma yi magana kan kashe-kashen da ake fama da su a wasu sassan ƙasar nan.
“Ko a kira shi kisan ƙare-dangi ko akasin haka, matsalar na shafarmu baki ɗaya. Ana kashe mutane ko ina,” in ji shi.
Ya jaddada cewa dole ne a haɗa kai don shawo kan matsalar.
“Shi ya sa ya zama dole mu yi aiki tare. Idan muka bar giɓi, su ne za su samu wajen shiga. Ba sa damuwa da wanda za su kashe. Waɗannan mutane mugaye ne, da yawa daga cikinsu ma suna shan miyagun ƙwayoyi.
“Saboda haka dole a kawo ƙarshen kashe-kashen nan. Manufarmu ita ce mu fuskance su kai-tsaye mu kuma dakatar da waɗannan kashe-kashen.”