Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-06@12:07:48 GMT

Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?

Published: 6th, December 2025 GMT

Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?

Yanzu ƴan Najeriya za su iya cire naira 100,000 ta na’urar cire kuɗi ta ATM a rana, haka ma abin yake a ɓangaren cire kuɗi ta na’urar POS.

A ɓangaren ma’aikatu kuma, za su iya cire kuɗi har naira miliyan biyar ne a duk mako.

Wannan na ƙunshe ne a cikin sabbin tsare-tsaren da Babban Bankin Najeriya CBN ya fitar bayan garambawul da ya yi kan dokokin cire kuɗi ta na’urar ATM da POS a Najeriya.

Bankin ya ce wannan sabuwar dokar za ta fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2026.

A cikin wata sanarwa da daraktan tsare-tsare na bankin, Dr Rita Sike ta fitar a ranar Talata 2 ga watan Disamba, ta ce babban bankin ya yi gyara ne a kan dokokin kuɗin da za a iya cirewa.

Amma idan mutum ya cire kuɗi sama da ƙa’idar da aka ƙayyade a mako, mutum zai biya wani adadi na kuɗin.

Ya kamata ƴan Najeriya su fahimci cewa ida suka shiga cikin banki suka cire naira 100,000, shi ma yana cikin kuɗin da suka cire a rana.

Hakan na nufin za a ƙirga shi a cikin kuɗin da mutum ya cire a makon, kamar ya cire ta ATM ko POS.

Me ya sa aka yi canjin?

Kamar yadda sanarwar ta nuna, an tsara tsohuwar dokar ce domin rage ta’ammali da tsabar kuɗi da magance matsalolin tsaro da ma daƙile sama da faɗi da kuɗaɗe da sauran abubuwan da ake tunanin ba su da sauƙi sai da tsabar kuɗi.

Sauran dokokin sun haɗa da:

Cire kuɗi mai yawa – Idan ka cire kuɗi sama da adadin da ƙayyade, za ka biya kashi uku, idan kuma ma’aikata ce za ta biya kashi biyar na kuɗin.

Amfani da takardar karɓar kuɗi a banki – Idan ka tura wani da takardar karɓar kuɗi wato ‘check’, shi ma za a ƙirga a cikin adadin kuɗin da ka cire a mako.

Yadda aka fara dokar

A watan Disamban 2022 ne babban bankin Najeriya ya sanar da cewa daga ranar 9 ga wata Janairun 2023, ɗaiɗaikun mutane ba za su cire kuɗi sama da naira 100,000 ba, ma’aikatu kuma naira 500,000.

Sannan a lokacin bankin ya ce adadin kuɗin da za a iya cirewa ta na’urar POS shi ne naira 20,000.

Haka kuma a lokacin bankin ya ƙayyade cewa ƙananan takardun kuɗi irin su naira 200 zuwa ƙasa ne za a riƙa sakawa a ATM.

Bankin ya fitar da tsare-tsaren ne bayan fitar da sababbin takardun kuɗi a Najeriya.

Idan mutum zai cire sama da adadin, zai biya kashi biyar, ma’aikatu kuma za su biya kashi 10.

A baya, kuɗin da mutum zai iya cirewa ta na’urar ATM naira 100,00 ne a mako, amma mutum naira 20,000 kawai zai iya cira a kullum, amma a POS kuma, naira 20,000 kawai za a iya cirewa.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cirewa za a iya cirewa naira 100 00

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ta ce ta samu rahoton laifuka 25 na cin zarafin mata da ƙananan yara a Ƙananan Hukumomin Jakusko, Fika, Potiskum da Tarmuwa, inda aka kama mutum 28 da ake zargi da aikata laifukan.

Kakakin rundunar, SP Abdulkarim Dungus, ya ce an kama masu laifin ne cikin watanni uku da suka wuce, a wani yunƙuri na daƙile cin zarafin mata da yara a faɗin jihar.

Tinubu ya san dalilin da ya sa na yi murabus daga muƙamin ministan — Badaru Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani matashi mai shekara 23, Yusuf Garba, da ake zargi yi wa wata yarinya mai shekaru biyar fyaɗe.

An kai yarinyar asibiti sannan ana ci gaba da bincike a kan lamarin.

A wani lamari daban, an yi wa wata yarinya mai shekara 16 fyaɗe yayin da ta ke dawowa gida daga bikin Maulidi a Babbangida.

’Yan sanda sun kama mutum biyu; Audu Ado (22) da Babangida Alhaji Dawaye, inda suka amsa laifin bibiyar yarinyar har suka yi mata rauni.

Dungus, ya ce waɗanda abin ya shafa na samun kulawa, yayin da ake ci gaba da bincike a ofishin SCID kafin gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Ado, ya la’anci waɗannan mummunan laifuka, inda ya bayyana cewa rundunar za ta gabatar da rahoton bincikenta kafkn gurfanar da waɗanda ake zargin.

Ya kuma shawarci iyaye, shugabannin al’umma da ƙungiyoyi su ƙara kula da yara tare da haɗa kai da ’yan sanda domin kare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dorinar ruwa ta kashe mutum 2, ta jikkata 6 a Gombe
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000