Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
Published: 6th, December 2025 GMT
Wasu mutane uku sun rasu yayin da suke tsaka da aikin yasar rijiya a garin Badume da ke Ƙaramar Hukumar Bichi a Jihar Kano.
A yayin da suke aikin haƙar rijiya, ɗaya daga cikinsu ya shiga domin yasowa biyu kuma na janyo ƙasar da aka haƙo.
Ana cikin haka igiyar ta tsinke, inda nan take ƙasa ta koma kan dattijon mai shekara 65 da ke haƙar rijiyar.
Hakan ya sa ɗansa mai shekara 20 shiga rijiyar domin fito da shi amma abu ya tura.
A nan ne na ukunsu mai 60 Yakubu Abdullahi shi ma ya shiga domin ceto su, amma duka dai abu ya gagara.
A ƙarshe jami’an Hukumar Kashe Gobara sun yi nasarar ceto su ukun a sume, amma daga baya likita ya tabbatar da rasuwarsu bayan kai su asibiti kamar yadda mai magana da yawun rundunar ya bayyana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: rijiya
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
Amurka ta faɗaɗa yawan ƙasashen da ta sanyawa haramcin samun bizar shiga ƙasar zuwa 32 ƙarƙashin jagorancin Donald Trump da ke tsaurara matakan shiga wannan ƙasa ta yammacin duniya saboda abin da ya kira barazanar ƙasashen ga tsaron Washington da kuma kange kwararar ƴan cirani.
Sakatariyar tsaron cikin gida ta Amurka Kristi Noem yayin wasu kalamanta a shirin kai tsaye ta gidan talabijin, ta ce dole ne Amurka ta dakatar da bizar ga duk wata ƙasa da ke turo mata baragurbi waɗanda ke wargaza tsaro da zaman lafiyarta.
Duk da cewa Noem bata bayyana sunayen ƙasashen ba, amma wasu bayanai da suka fita daga ma’aikatar sirrin ƙasar sun ce galibinsu ƙasashe ne na Afrika ciki kuwa har da Kenya da Angola da Masar da Habasha da Ivory Coast sai kuma Najeriya a gaba-gaba.
Wasu majiyoyi sun ce, daga cikin dalilan da ya sanya Amurka saka haramcin visa kan ƙasashen har da yadda wasunsu suka ƙi amincewa da karɓar ƴanciranin da Washington ke tisa ƙeyarsu, sai kuma batutuwa masu alaƙa da rashin isassun takardun shaida daga ƴan ƙasashen kana rashin inganci fasfo.
A cewar Noem yanzu haka ana ci gaba da tantance waɗannan ƙasashe don fitar da jerinsu, matakin da ke zuwa bayan tun a ranar 28 ga watan Nuwamban da ya gabata shugaba Trump ya sanya haramci visa kan mutanen da ke shigowa Amurkan daga ƙasashe matalauta ko masu fama da yaƙi.
Matakin na Amurka na zuwa bayan harin ranar 26 ga watan na jiya, da ya kai ga kisan wani Soja guda, harin da ake zargin wani ɗan ƙasar Afghanistan da kaiwa wanda aka ce ya shiga Amurkan don neman mafaka a shekarar 2021.
Ko a watan Yuni Amurka ta sanya haramcin visa kan ƙasashen Chadi da Congo da Equatorial Guinea da kuma Eritrea baya ga Libya da Somalia da kuma Sudan.
A wani mataki na daban kuma gwamnatin ta Amurka ta buƙaci tsauri kan matafiyan da ke shiga ƙasar daga Burundi da Saliyo da kuma Togo.