Aminiya:
2025-12-13@13:22:55 GMT

Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi

Published: 3rd, December 2025 GMT

Majalisar Wakilai za ta ƙada kuri’a a ranakun 10 da 11 ga watan Disamba kan muhimman kudurorin gyaran kundin tsarin mulkin 1999, ciki har da kirkirar sabbin jihohi da kafa ’yan sandan jihohi.

Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Okezie Kalu, ya sanar da jadawalin a zaman majalisar, inda ya ce tattaunawa kan kudirin sauya kundin tsarin mulki za ta gudana yau da gobe kafin kada kuri’ar mako mai zuwa.

An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya

Kalu, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan nazarin kundin tsarin mulki, ya bukaci ’yan majalisa su halarci zaman.

Ya shaida wa majalisar kwanan nan cewa kwamitin ya kammala aikin da ake bukata a wannan mataki, kuma yana shirin gabatar da takardun da aka daidaita don a yi la’akari da su.

A farko dai an gabatar da jimillar kudirori 87 da ke neman sauya sassa daban-daban na kundin tsarin mulki.

Kudirorin sun shafi gyaran harkokin zabe da shari’a, ’yan sandan jihohi da batutuwan kudi.

Sai dai bayan jin ra’ayin jama’a a matakin jihohi, taron jin ra’ayin jama’a na kasa a Abuja, tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma daidaitawa da kwamitin majalisar dattawa kan kundin tsarin mulki, adadin kudirin da za a kada kuri’a ya ragu zuwa kusan 45.

A ranar Litinin, 24 ga watan Nuwamba, kwamitocin majalisar wakilai da na majalisar dattawa kan gyaran kundin sun gudanar da taron hadin gwiwa da kakakin majalisun jihohi a Abuja yayin da tsarin sauya kundin ya shiga matakin karshe.

Kalu da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, sun shaida wa kakakin majalisun jihohi cewa makomar kudirin sauye-sauyen yanzu ta dogara ne da majalisun jihohi bayan majalisar tarayya ta kammala aikinta. Kalu ya ce taron ya nuna matakin karshe kafin fara kada kuri’a.

Muhimman kudirorin da ake son gyarawa

Daga cikin muhimman sauye-sauyen da aka gabatar kirƙirar ’yan sandan jihohi, ware kujeru na musamman ga mata a majalisa, ’yancin tsayawa takara ba tare da jam’iyya ba, karin ayyuka ga sarakunan gargajiya, karfafa ikon majalisar tarayya da ta jihohi wajen kira shugaban ƙasa da gwamnonin jihohi kan harkokin tsaro da sauransu.

Kazalika, wani kudiri na neman sauya kundin domin mayar da gudanar da zaben kananan hukumomi daga hukumar zabe ta jihohi zuwa INEC.

Haka kuma, wani kudiri na neman tabbatar da cewa a kammala dukkan shari’un zabe kafin rantsar da zababbun jami’ai.

Babban kudiri kuma shi ne na neman kafa ’yan sandan jihohi ta hanyar sauya kundin tsarin mulki domin cire su daga jerin dokokin tarayya zuwa jerin dokokin hadin gwiwa.

Masu goyon baya sun ce wannan mataki zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da suka yi yawa kuma suke neman fin ƙarfin ’yan sandan tarayya.

Kallo zai koma majalisun jihohi

Bayan an kammala kada kuri’a, za a tura kudirin da aka amince da su zuwa majalisun jihohi 36 don samun amincewa.

Aƙalla majalisun jihohi 24 (wato kashi biyu bisa uku) dole ne su amince da shi kafin a tura su ga shugaban ƙasa don ya sanya hannu.

Duk kudirin da bai samu amincewar jihohi ba zai mutu nan take.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakikai kundin tsarin mulki yan sandan jihohi sauya kundin

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar bunkasa ilimin manya ta jihar Jigawa tace za ta kashe naira milyan 400 wajen gudanar da harkokin ta a sabuwar shekara ta 2026.

Shugaban hukumar. Dr. Abbas Abubakar Abbas, ya bayyana haka lokacin kare kiyasin kasafin kudin hukumar a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Dr Abbas Abubakar Abbas ya ce hukumar za ta yi amfani da kudaden wajen inganta shirye shiryen koyon karatu da rubutu ga manya maza da mata da na ci gaba da karatu don kammala karatun sakandare da na masu son sake jarrabawar sakandire da koyon karatu ta Rediyo da cibiyoyi daban daban da ke fadin jihar.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumarsa , shugaban hukumar makarantun Tsangaya, Dr. Hamisu Maje, ya ce sun yi kiyasin naira milyan dubu 3 da milyan 500 tare da kudurin kammala aikin ginin makarantun Tsangaya guda 3 da ke Ringim da Kafin Hausa da Dutse.

Ya ce an yi tanadi domin kafa cibiyar koyar da sana’oi da gidajen alarammomi da masallaci tare da samar da ruwan sha da wutar lantarki a kowacce makaranta.

Dr. Hamisu Maje ya kuma bayyana cewar hukumar za ta gyara makarantun Tsangaya guda 7 da aka gada daga gwamnatin tarayya da ke sashen jihar domin karfafa tsarin ilimin makarantun Tsangaya na zamani.

A daya bangaren kuma, kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse da Kuma hukumar bada tallafin karatu ta jihar sun kare kiyasin kasafin kudadensu a gaban kwamatin kula da manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Da ya ke kare kiyasin kasafin kudin, shugaban kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse, Dr. Ahmad Badayi, ya ce sun yi kiyasin fiye da naira milyan 700 wadda daga ciki an kebe naira milyan 330 domin sayo kayayyakin aiki a dakin gwaje-gwaje da koyon aikin hannu da gyaran ofisoshi, yayin da za a yi amfani da ragowar kudaden wajen kammala manyan ayyuka.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumar sa, shugaban hukumar bada tallafin karatu ta jihar Malam Sa’idu Magaji, ya ce sun yi kiyasin kashe naira milyan dubu 10 domin bada tallafin karatu na cikin gida da na kasashen waje.

A nasa jawabin, shugaban kwamatin kula da ilimin manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Sule Tankarkar Alhaji Muhammad Abubakar Sa’id, ya jaddada bukatar ganin masu ruwa da tsaki a bangaren manyan makarantu sun yi dukkan mai yiwuwa domin inganta harkokin ilimi mai zurfi a sabuwar shekara.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na  Venuzuela
  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye