Aminiya:
2025-12-05@19:19:11 GMT

Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike

Published: 5th, December 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa har yanzu yana nan daram a jam’iyyar PDP.

Ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Juma’a yayin da yake mayar da martani kan ficewar wasu ’yan majalisar dokoki na Jihar Rivers daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.

8 cikin watanni 15

A ranar Juma’a, ‘yan majalisar Ribas guda 16, ciki har da Kakakin Majalisar, Martins Amaewhule, da suka sauya sheƙa zuwa APC.

Amaewhule, ya ce ya yanke shawarar komawa APC ne saboda rarrabuwar kai da aka samu a PDP.

Hakazalika, kakakin ya ce yana son ya yi aiki tare da Shugaba Bola Tinubu, bayan ya gano yana da kyakkyawan tsari na ciyar da ƙasar nan gaba.

Da yake magana da manema labarai bayan duba wasu ayyuka a Abuja, Wike, ya ce ’yan majalisun ba su tuntuɓe shi game da batun sauya sheƙarsu ba, amma ya ce suna da  ’yancin zaɓen abin da suke so.

Ya ƙara da cewa ba duka ’yan majalisar ne suka fice daga PDP ba.

Ya ce, “Ni har yanzu ina PDP. Ba dukkaninsu ne suka fice daga jam’iyyar PDP ba. Ina ganin 16 ko 17 ne suka fice daga cikin 27. Har yanzu muna da kusan mutum 10, kuma za mu ci gaba da aiki tare da su.”

Wike, ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, amma ya ce kowa na da ’yancin zaɓen abin da yake so.

Ya ɗora alhakin ficewarsu kan rikicin cikin gida da PDP ke fama da shi, inda ya bayyana cewa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya bai wa mutane damar barin jam’iyyar idan ta rabu gida biyu.

Ya ce tun da farko ya bai wa shugabancin PDP shawara su gyara jam’iyyar, tare da gargaɗin cewa idan ba a ɗauki mataki ba jam’iyyar za ta ci gaba da yin asara.

Wike, ya ƙara da cewa suna ci gaba da ƙoƙari domin sauran mambobin PDP su haɗa kai don yaƙar jam’iyyun adawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan majalisa Babban Birnin Tarayya Siyasa yan majalisar a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina

Wata gobara da ta tashi da safiyar Litinin ta kashe magidanci da matarsa da ’ya’yansa uku a unguwar Kofar Sauri da ke cikin garin Katsina.

Wadanda gobarar ta rutsa da su sun haɗa da Muhammad Habibu mai shekara 35, matarsa Fatima Muhammad, da ’ya’yansu uku; Khadija, Abubakar, da Aliyu, wadanda dukkansu suka ƙone har lahira.

Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro

Gobarar ta kuma lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

An gano cewa Muhammad Habibu ma’aikaci ne na wucin gadi a hukumar ruwa ta jihar Katsina kafin rasuwarsa.

Kodayake ba a tabbatar da ainihin dalilin gobarar ba tukuna, mazauna yankin suna zargin ta faru ne sakamakon tashin wuta mai ƙarfi lokacin da aka dawo da lantarki a yankin.

An ce gobarar ta fara ne daga falon gidan sannan ta bazu cikin sauri zuwa sauran sassan gidan, yayin da iyalin ke tsaka da sharer barci.

Bayanai sun ce lokacin da suka fahimci hatsarin, wutar ta riga ta toshe dukkan hanyoyin fita.

Ɗan uwa ga waɗanda suka rasu, Kasim Aliyu, ya ce da misalin ƙarfe 3:00 na safe ya ji muryar wata mace daga nesa tana karanta kalmar shahada: “Innalillahi wa inna ilayhi raji’un.” Da farko ya ɗauka al’ada ce, sai da misalin ƙarfe 3:30 na safe ya fara jin akwai matsala.

Kasim ya ƙara da cewa: “Mai gidan ƙanina ne ubanmu ɗaya. Gobarar ta kama gidan da misalin ƙarfe 3:00 na safe. Na ji wani abu a lokacin amma ban gane ba sai da aka kira ni da misalin ƙarfe 4:00 na safe aka shaida min cewa ƙanina da iyalinsa gaba ɗaya sun mutu a gobarar. Allah ya jikan su.”

Shaidun gani da ido sun ce ƙoƙarin makwabta da masu taimakon gaggawa wajen kashe gobarar ya ci tura.

Sun yi korafin cewa jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Katsina sun iso daga baya amma zuwan nasu bai yi wani tasiri ba sosai.

Wani mazaunin yankin, Musa Hamza, ya ce: “Ina ganin lokacin da hukumar kashe gobara ta iso, mutanen cikin gidan sun riga sun mutu a gobarar. Amma zan iya cewa sun yi iya ƙoƙarinsu wajen kashe wutar, sai dai ba su samu nasarar ceto iyalin ba. Allah ya jikan su.”

Wani makwabci, Magaji Bala, ya yi korafi cewa mazauna yankin sau da yawa suna shafe kwanaki ba tare da lantarki ba, sai kuma tashin wuta mai ƙarfi ya jawo barna duk lokacin da aka dawo da wuta.

“Irin wannan lamari ya taɓa faruwa a wasu sassan garin Katsina. Kwanan nan ma kusan irin haka ya faru. Wannan ya sa dole mutane su yi taka-tsantsan,” in ji shi.

Da aka tuntubi Babban Jami’in Kashe Gobara na jihar Katsina, Rabe Audi Kurmuyal, ya tabbatar da cewa ma’aikatansa sun kashe gobarar, sabanin ikirarin da ake yi cewa sun iso daga baya.

Wasu mazauna sun dora laifin kan matsalar sauyin wuta da ake yawan samu daga kamfanin rarraba na shiyyar Kano (KEDCO), suna cewa yawan katsewa da dawowa da ƙarfin lantarki mai yawa na lalata kayan lantarki.

Sai dai kamfanin ya musanta zargin, inda ya ca ba zai yiwu a ce laifinsu ba ne, kasancewar gidan shi kadai ya kone a unguwar mai gidaje sama da 5,000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya
  • Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
  • MDD ta bukaci a kawo karshen mamayar Isra’ila a Falasdinu da kuma janyewa daga Tuddan Golan na Siriya
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Sabon Shugaban Hukumar Kidaya, Kwamishinoni da Manyan Sakatarori
  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro