Mutane 62 da aka sace sun tsere daga hannun ’yan bindiga a Katsina
Published: 19th, August 2025 GMT
Mutum 62 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su sama da wata guda sun tsere bayan rundunar soji ta kai farmakin sama da ƙasa a maboyar ’yan ta’adda a Karamar Hukumar ƊanMusa, Jihar Katsina.
Farmakin da aka kai a ranar Asabar da misalin ƙarfe 5:10 na yamma ya gudana ne bisa sahihan bayanan leƙen asiri, inda dakarun sojin sama da na ƙasa suka haɗa kai wajen kai hari a kauyen Jigawa Sawai, wanda ke iyaka da Jihar Zamfara.
A cewar sanarwar da Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Katsina ta fitar, farmakin ya tilasta ’yan bindigar guduwa, lamarin da ya ba wa mutanen da aka yi garkuwa da su damar tserewa cikin ruɗani.
Wasu daga cikin waɗanda suka tsere sun bayyana cewa sun rabu da juna yayin tserewa, amma an tattaro su daga sassa daban-daban.
Lafiyata garau, ba jinya ta kai ni London ba — Akpabio Sojoji sun kwace makamai 2,000 a shekara gudaGwamnatin jihar ta ce mafi yawan waɗanda aka ceto an sace su ’yan asalin ƙauyen Sayaya a Ƙaramar Hukumar Matazu, a wani farmaki da aka kai da daddare ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, daga wani gungun ’yan bindiga da ake kira na Muhammadu Fulani.
A halin yanzu, mutum 12 daga cikin waɗanda suka tsere suna samun kulawar likita a Asibitin Matazu, yayin da 16 ke a sansanin soji na Kaiga Malamai. Ana ci gaba da tantance lafiyar sauran kafin a haɗa su da iyalansu.
Kwamishinan Tsaro, Nasir Mu’azu, ya bayyana cewa an tura Sojin Sama zuwa ƙananan hukumomin Matazu da Bakori domin dakile hare-haren ’yan bindiga da kuma tabbatar da zaman lafiya.
Gwamna Dikko Radda ya yaba da ƙwazon jami’an tsaro, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa na da niyyar kawo ƙarshen ta’addanci a jihar.
Ya kuma tabbatar wa iyalan waɗanda aka ceto cewa za a haɗa su da ’yan uwansu bayan an kammala duk wasu bincike da jinyar da ake yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp