Ya soka wa budurwarsa wuka har lahira
Published: 19th, August 2025 GMT
Wani mutum ya soka wa budurwarsa mai suna “Ima” wuka har lahira a unguwar Okereke Street da ke garin Fatalkwal na Jihar Ribas.
Mutumin, wanda ake wa lakabi da “Doctor” ya daba wa budurwar tasa mai suna “Ima” wuka ne bisa zargin tana cin amanarsa.
Lamarin ya faru ne da yammacin Lahadi, wanda shaidu a unguwar suka ce ya samo asali ne daga zargin da Doctor ke yi wa Ima, wanda ya rikide zuwa tashin hankali.
Mai kula da gidan da lamarin ya faru ya kai rahoto ofishin’yan sanda na Azikiwe Division, Mile 2 Diobu, wanda hakan ya kai ga cafke wanda ake zargi.
’Yan bindiga sun yi hatsari bayan karbar kudin fansa Mutane 62 da aka sace sun tsere daga hannun ’yan bindiga a KatsinaRahotanni sun nuna cewa an kai gawar zuwa wani gidan ajiyar gawa da ba a bayyana ba a Fatakwal.
Prince Wiro, Shugaban Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam da Inganta Gaskiya, ya bukaci a gudanar da bincike mai zurfi da adalci.
Ya ce, “Mun ga yadda aka dauke gawar zuwa gidan ajiyar gawa yayin da ake tsare wanda ake zargi. Muna kira ga ’yan sanda da su gudanar da bincike mai adalci domin tabbatar da gaskiya.”
Ya kuma shawarci matasa da su guji dangantaka mai cike da tashin hankali: “Ba a bukatar mutum ya zauna cikin dangantaka mai cutarwa. Rayuwarka ta fi kowace dangantaka muhimmanci.”
Kakakin ’yan sanda na Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ba ta amsa kiran waya ko sakon da aka tura mata dangane da lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: budurwa masoya Masoyiya zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Shugaba Xi ya kara da cewa, a halin da ake ciki yanzu, duniya na fuskantar sauye-sauye irin wadanda ba a taba gani ba kuma cikin sauri. Don haka, kamata ya yi kasashen biyu masu dadaddun wayewar kai su zurfafa koyi da juna, da shigar da sabon kuzari cikin gina cikakken salon hadin kai, bisa manyan tsare-tsare tsakaninsu, kana su tattaro karfin wayewar kai don gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.
A wani ci gaban kuma, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping wato ministan raya al’adu da yawon bude ido na kasar Sun Yeli, ya halarci bikin bude babban gidan adana kayan tarihin na GEM bisa gayyatar gwamnatin Masar. Kafin bikin, shugaba al-Sisi ya gana tare da gudanar da gajeriyar tattaunawa da Sun Yeli. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA